DNN Hausa

DNN Hausa DNN News Hausa: Sahihan Labarai Da Ɗumi-Ɗumi | Bincike | Siyasa | Shirye-Shirye Na Musamman | Da Labaran Wasanni Da na Nishaɗi.
(1)

Ku na iya tuntuɓarmu kai tsaye: 08061341152

Zan cigaba da yin addu'a kan a samu haɗin kai tsakanin yan Najeriya har zuwa lokacin da zan mutu - Uzor Kalu, tsohon Gwa...
23/06/2026

Zan cigaba da yin addu'a kan a samu haɗin kai tsakanin yan Najeriya har zuwa lokacin da zan mutu - Uzor Kalu, tsohon Gwamnan jihar Abia.

"Idan ba'a haɗa maka da Kuɗin masu Kidnapping ba to za'a siyar da gidan ku a karbo ka ko matar"Sheikh Ahmad Yusuf Gurunt...
23/06/2026

"Idan ba'a haɗa maka da Kuɗin masu Kidnapping ba to za'a siyar da gidan ku a karbo ka ko matar"

Sheikh Ahmad Yusuf Guruntum, Malamin Islama.

Gwamnatin Jihar Kaduna ta bayyana goyon bayan ta ga matakin gurfanar da mutane 24 da ake zargi da hannu a kisan gillar d...
23/06/2026

Gwamnatin Jihar Kaduna ta bayyana goyon bayan ta ga matakin gurfanar da mutane 24 da ake zargi da hannu a kisan gillar da aka yi wa wata mata a yankin Maraban Jos, tana mai cewa hakan wani muhimmin mataki ne wajen tabbatar da adalci da kuma mutunta doka.

A cikin wata sanarwa da Kwamishinan Yaɗa Labarai da Al’adu na jihar, Ahmed Maiyaki, ya fitar a ranar Talata, gwamnatin ta yabawa rundunar ‘yan sandan jihar bisa gaggawar da ta yi wajen daukar mataki kan lamarin da ya janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin al’umma.

Gwamnatin Amurka ta ayyana wani ɗan Najeriya tare da wasu mutane da kamfanoni a Turai, Gabas ta Tsakiya da Afirka ta Yam...
23/06/2026

Gwamnatin Amurka ta ayyana wani ɗan Najeriya tare da wasu mutane da kamfanoni a Turai, Gabas ta Tsakiya da Afirka ta Yamma a matsayin waɗanda ake zargi da taimaka wa ƙungiyar ta'addanci ta ISIS wajen gudanar da harkokin kuɗaɗen ta.

A wata sanarwa da Ma'aikatar Harkokin Wajen Amurka ta fitar, mai magana da yawunta, Thomas Pigott, ya ce matakin ya shafi mutum uku da kamfanoni shida da ake zargi da taka muhimmiyar rawa wajen sauƙaƙa safarar kuɗaɗe domin ayyukan ISIS a sassa daban-daban na duniya.

Sai dai sanarwar ba ta bayyana cikakken sunan ɗan Najeriyar ko ƙarin bayanai game da sauran mutanen da abin ya shafa ba zuwa lokacin fitar da rahoton.

Gwamnatin mulkin sojin Jamhuriyar Nijar ta mika takardar ta a hukumance domin ficewa daga Kotun Hukunta Manyan Laifuka t...
23/06/2026

Gwamnatin mulkin sojin Jamhuriyar Nijar ta mika takardar ta a hukumance domin ficewa daga Kotun Hukunta Manyan Laifuka ta Duniya (ICC), watanni tara bayan sanar da wannan aniya tare da kasashen Mali da Burkina Faso.

Kotun ICC mai hedikwata a birnin Hague na kasar Netherlands ta tabbatar da cewa ta karbi sanarwar ficewar Nijar a ranar 18 ga Yunin 2026.

Tun a watan Satumban shekarar 2025 ne gwamnatin Nijar karkashin jagorancin Janar Abdourahamane Tiani, tare da Mali da Burkina Faso, s**a bayyana aniyarsu ta janye daga kotun, suna zargin ta da kasancewa wata kafa da kasashen yamma ke amfani da ita wajen nuna wariya da danniya.

A cewar ICC, ficewar Nijar ba za ta fara aiki ba sai ranar 18 ga Yunin 2027, shekara guda bayan gabatar da takardar sanarwar, kamar yadda dokokin kotun s**a tanada.

Sai dai kotun ta bayyana cewa har zuwa lokacin da ficewar za ta fara aiki, Nijar za ta ci gaba da cika dukkan sharadai da nauye-nauyen da s**a rataya a wuyan ta a matsayinta na mambar kotun.

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bukaci dukkan sanatoci su tabbatar da halartar zaman majalisar n...
23/06/2026

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, ya bukaci dukkan sanatoci su tabbatar da halartar zaman majalisar na ranar Laraba domin kada kuri’a kan kudirin gyaran kundin tsarin mulki da ke neman kafa rundunar ‘yan sandan jihohi a fadin Najeriya.

Akpabio ya bayyana kudirin a matsayin daya daga cikin muhimman sauye-sauyen da za su iya canja tsarin tsaro a kasar, yana mai cewa lokaci ya yi da za a bai wa jihohi damar taka rawa kai tsaye wajen kula da harkokin tsaro.

Yayin zaman gaggawa na Majalisar Dattawa da aka gudanar ranar Talata, shugaban majalisar ya ce kafa ‘yan sandan jihohi zai taimaka wajen magance matsalolin rashin tsaro da s**a hada da ta’addanci, garkuwa da mutane da ayyukan ‘yan bindiga.

'Yan bindiga sun yi garkuwa da mata da kuma ɗan Shugaban Jam'iyyar APC na Ƙaramar Hukumar Yauri ta jihar Kebbi wato Alha...
23/06/2026

'Yan bindiga sun yi garkuwa da mata da kuma ɗan Shugaban Jam'iyyar APC na Ƙaramar Hukumar Yauri ta jihar Kebbi wato Alhaji Yusuf Alhasan.

Rahotanni daga garin na Yauri sun nuna cewa maharan sun kai hari zuwa gidan sa da ke Unguwar Low-Cost da tsakar daren Lahadi zuwa safiyar Litinin, inda s**a yi awon gaba da matar da ɗansa.

Kawo yanzu dai babu wani bayani akan halin da suke ciki.

Gwamnatin Iran ta ayyana hutun kwana uku a birnin Tehran domin gudanar da jana'izar marigayi Jagoran Addini na ƙasar, Ay...
23/06/2026

Gwamnatin Iran ta ayyana hutun kwana uku a birnin Tehran domin gudanar da jana'izar marigayi Jagoran Addini na ƙasar, Ayatollah Ali Khamenei.

Rahotannin kamfanin dillancin labarai na AFP sun ce an ɗauki matakin ne domin bai wa al'umma damar halartar jana'izar tare da gudanar da makokin rasuwar jagoran.

Ana sa ran dubban mutane daga sassa daban-daban na ƙasar za su halarci jana'izar, yayin da hukumomi ke ci gaba da shirye-shiryen gudanar da taron cikin tsari da kwanciyar hankali.

Rasuwar Khamenei ta zo a ranar 28 ga watan Fabrairu yayin yaƙin da Amurka da Isra'ila s**a kaddamar kan Iran.

Gwamnatocin Najeriya da Burtaniya sun sake jaddada aniyarsu ta karfafa hadin gwiwa wajen yaki da daukar nauyin ta’addanc...
23/06/2026

Gwamnatocin Najeriya da Burtaniya sun sake jaddada aniyarsu ta karfafa hadin gwiwa wajen yaki da daukar nauyin ta’addanci, laifukan intanet, yada bayanan karya da sauran barazanar tsaro da ke tasowa a duniya.

An bayyana hakan ne yayin taron tattaunawar hadin gwiwar tsaro da kariya tsakanin kasashen biyu karo na hudu da aka gudanar a Abuja.

Mai bai wa Shugaban Kasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu, ya ce hadin gwiwar ya fadada daga yaki da ta’addanci zuwa fannoni da s**a hada da tsaron intanet, tsaron teku, musayar bayanan sirri, magance rikice-rikice da tabbatar da zaman lafiya a yanki.

A nasa jawabin, mai bai wa gwamnatin Birtaniya shawara kan harkokin tsaro, Jonathan Powell, ya bayyana Najeriya a matsayin babbar abokiyar hadin gwiwar Birtaniya a Afirka kuma ginshiki wajen tabbatar da tsaron yankin.

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya aika wa Majalisar Dattawa kudirin gyaran kundin tsarin mulkin Najeriya domin samar ...
23/06/2026

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya aika wa Majalisar Dattawa kudirin gyaran kundin tsarin mulkin Najeriya domin samar da tsarin kafa ‘yan sandan jihohi.

Kudirin na neman yin gyara ga wasu tanade-tanaden Kundin Tsarin Mulkin shekarar 1999 domin samar da cikakken tsarin doka da zai bai wa jihohi damar kafa rundunonin ‘yan sanda nasu na kan su.

Matakin na zuwa ne bayan kiraye-kirayen da aka dade ana yi kan bukatar bai wa jihohi karin iko wajen tafiyar da harkokin tsaro domin magance matsalolin ta’addanci, garkuwa da mutane da sauran laifuffuka da s**a addabi sassan kasar nan.

Tun a watan Fabrairu, Shugaba Tinubu ya bukaci Majalisar Tarayya ta yi gyaran kundin tsarin mulki domin samar da damar kafa ‘yan sandan jihohi, yana mai bayyana cewa hakan zai taimaka wajen inganta yaki da matsalolin tsaro a fadin kasar.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DNN Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Establishment

Send a message to DNN Hausa:

Share