10/05/2026
Lokacin Matasa Ne Ya Kamata A Gina Lahira Da Kyawawan Ayyuka Kafin Tsufa -Sheikh Abdulhameed Bello Zaria
Daga Abubakar Sani Batsari
A safiyar ranar Asabar, 9 ga Mayu, 2026, Dandalin Matasan Harkar Musulunci na Imam Husain (AS) Zone Katsina ya ci gaba da gudanar da taron ƙara wa juna sani karo na biyu, wanda ke gudana a garin Batsari da ke Jihar Katsina.
Yayin gabatar da maudu’i na farko mai taken “Hadafin Harka Islamiyya da Kuma Hadafin Halittar Ɗan Adam”, Sheikh Abdulhameed Bello Zaria ya bayyana cewa manufar gwagwarmayar addinin Musulunci ita ce ceto ɗan Adam daga azabar wuta zuwa aljanna.
Ya ce matasa su ne ƙashin bayan al’umma, don haka lokaci ne da ya dace su yi amfani da ƙarfinsu wajen gina lahirarsu da kyawawan ayyuka kafin tsufa.
“Lokacin matasantaka lokaci ne da ya kamata matashi ya fahimci ni’imar da Allah SWT Ya yi masa, tare da amfani da ita wajen bautar Allah da kyautata ayyuka,” in ji Sheikh Abdulhameed.
A maudu’i na biyu mai taken “Wajibcin Neman Ilimi da Hanyoyin Samunsa”, Dr. Shu’aibu Muhammad Gashua ya jaddada muhimmancin neman ilimi a rayuwar Musulmi.
Ya ambato maganar Imam Ali (AS) da ke cewa: “Neman ilimi ya fi zama wajibi a kanku fiye da neman dukiya.”
Dr. Gashua ya ƙara da cewa idan mutum ya haɗa ilimi da aiki da shi, hakan kan kai shi ga babban matsayi har mala’iku su riƙa ambaton sunansa a sama.
Haka kuma, a maudu’i na uku mai taken “Neman Aure da Zamantakewar Iyali a Manhajin Ɗan Gwagwarmaya”, Malama Khadija Katsina ta yi bayani kan yadda tsarin aure a Musulunci ya kamata ya kasance.
Ta ce Musulunci bai yarda a yi aure ba tare da fahimta da tattaunawa tsakanin ma’aurata ba, tare da ƙarfafa zaɓen abokin zama mai addini, kamala da ilimi.
A maudu’i na huɗu kuwa, Sheikh Hamza Musa Wagini ya gabatar da jawabi mai taken “Kyawawan Ɗabi’u Makamin Ɗan Gwagwarmaya Zuwa Ga Nasara”.
Ya bayyana cewa akwai buƙatar matashi ya suffanta kansa da kyawawan ɗabi’u har su zama jiki da jini a rayuwarsa.
“Ya zama wajibi mutum ya gyara mu’amalarsa da Allah SWT da kuma hulɗarsa da mutane, ba tare da jin cewa ya fi wani ba,” in ji shi.
Sheikh Wagini ya kuma jaddada muhimmancin kyautatawa iyaye, yana mai cewa duk wanda ya kyautata wa iyayensa, shi ma wata rana za a kyautata masa.
Tun da farko dai, bayan buɗe taron da addu’a, mawaƙan Matasan Harkar Musulunci sun gabatar da majalisi, sannan aka gudanar da salloli da liyafar cin abinci.
An bayyana cewa ana shirya taron ne domin gina shaksiyyar matasa ‘yan gwagwarmaya tare da ƙara kusanta su da harkar Musulunci.