DNN Hausa

DNN Hausa DNN News Hausa: Sahihan Labarai Da Ɗumi-Ɗumi | Bincike | Siyasa | Shirye-Shirye Na Musamman | Da Labaran Wasanni Da na Nishaɗi.
(1)

Ku na iya tuntuɓarmu kai tsaye: 08061341152

Da yake bayyana sakamakon zaɓen, shugaban kwamitin gudanarwa, Sanata Sani Danladi, ya ce Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami...
21/05/2026

Da yake bayyana sakamakon zaɓen, shugaban kwamitin gudanarwa, Sanata Sani Danladi, ya ce Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami ya samu kuri’u 12,120, yayin da tsohon Ministan Sufuri, Sanata Sa’id Ahmed Alkali, ya samu kuri’u 11,612.

Jam’iyyar APC reshen jihar Gombe ta bayyana Dr. Jamilu Isiyaku Gwamna a matsayin wanda ya lashe zaɓen fidda gwani na gwa...
21/05/2026

Jam’iyyar APC reshen jihar Gombe ta bayyana Dr. Jamilu Isiyaku Gwamna a matsayin wanda ya lashe zaɓen fidda gwani na gwamna da jam’iyyar ta gudanar domin tunkarar babban zaɓen shekarar 2027.

A cewar sanarwar da gwamnatin jihar ta wallafa, Dr. Gwamna ya samu kuri’u 247,161, lamarin da ya ba shi damar kayar da sauran masu neman takarar biyu da s**a shiga fafatawar.

Da yake bayyana sakamakon zaɓen, shugaban kwamitin gudanarwa, Sanata Sani Danladi, ya ce Farfesa Isa Ali Ibrahim Pantami ya samu kuri’u 12,120, yayin da tsohon Ministan Sufuri, Sanata Sa’id Ahmed Alkali, ya samu kuri’u 11,612.

An gudanar da zaɓen ne a hedikwatar jam’iyyar APC da ke jihar Gombe, tare da halartar jami’an Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ƙarƙashin jagorancin kwamishinan zaɓe na jihar, Alhaji Umar Mukhtar Gajiram.

Fadar Shugaban Ƙasa ta musanta rahotannin da ke yawo cewa shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, na shirin sauya sunan Najeri...
21/05/2026

Fadar Shugaban Ƙasa ta musanta rahotannin da ke yawo cewa shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, na shirin sauya sunan Najeriya zuwa “United States of Nigeria” tare da soke shari'ar Musulunci ta hanyar gyaran kundin tsarin mulki.

A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Alhamis, ya bayyana rahoton a matsayin ƙarya da aka ƙirƙira domin haddasa rikici da tayar da zaune tsaye kafin babban zaɓen 2027.

Sanarwar ta ce babu kamshin gaskiya a cikin ikirarin cewa Shugaba Tinubu na da niyyar yin wasu gyare-gyaren kundin tsarin mulki da za su sauya sunan Najeriya ko kuma su soke Shari’a a Arewa.

Sharri aka yi min.Me zaku ce ?
21/05/2026

Sharri aka yi min.

Me zaku ce ?

Kamfanin siminti na BUA ya bayyana cewa farashin siminti zai ragu ne kadai idan aka samu sauƙin farashin kayan da ake am...
21/05/2026

Kamfanin siminti na BUA ya bayyana cewa farashin siminti zai ragu ne kadai idan aka samu sauƙin farashin kayan da ake amfani da su wajen samar da shi da kuma kudin sufuri.

Shugaban kamfanin, Abdul Samad Rabiu, ya ce hauhawar farashin siminti a Najeriya ya samo asali ne daga tashin farashin dala, makamashi da sufuri, ba wai saboda neman riba mai yawa ba.

Ruwan sama ya sauka a Kano.
21/05/2026

Ruwan sama ya sauka a Kano.

Hukumar Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON) ta sanar da cewa ta kammala jigilar maniyyatan Najeriya zuwa ƙasar Saudiyya domin g...
21/05/2026

Hukumar Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON) ta sanar da cewa ta kammala jigilar maniyyatan Najeriya zuwa ƙasar Saudiyya domin gudanar da aikin Hajjin 2026, inda ta ce za a fara dawo da maniyyata gida daga ranar 3 ga watan Yuni.

A wata sanarwa da hukumar ta fitar ranar Alhamis, ta bayyana cewa jirgi na ƙarshe ya tashi da ƙarfe 10:44 na safe daga filin jirgin saman Gusau a Jihar Zamfara, ɗauke da maniyyata zuwa Saudiyya ta hannun kamfanin Max Air.

NAHCON ta ce aikin jigilar maniyyatan ya fara ne tun ranar 3 ga watan Mayu, kuma an kammala jigilar cikin kwanaki 18 kacal tare da jirage 98.

A cewar hukumar, Najeriya ta samu guraben aikin Hajji 50,000 a bana, ciki har da guraben da aka ware wa kamfanonin yawon Hajji masu lasisi da jami’an gudanarwa. Daga cikin adadin, an yi nasarar jigilar kusan maniyyata 39,000 na gwamnati zuwa ƙasar Saudiyya.

Sai dai hukumar ta bayyana cewa wasu daga cikin maniyyatan ba su samu damar tafiya ba sakamakon matsalolin rashin lafiya da kuma rasuwar wasu bayan an gama musu takardun biza.

Tsohon dan takarar shugabancin Najeriya a jam'iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi watsi da ikirarin da ke cew...
21/05/2026

Tsohon dan takarar shugabancin Najeriya a jam'iyyar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi watsi da ikirarin da ke cewa yana yiwa Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, aiki a ɓoye domin lashe zaɓen 2027.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da Global TV a daren Laraba, inda ya ce tun lokacin da yake jam’iyyar NNPP ake ta yaɗa irin wannan jita-jita.

Ya ce babu kamshin gaskiya a zargin, yana mai cewa mutane “sakarai” ne kawai zai yarda cewa yana yi wa Tinubu aiki ta bayan fage.

Kalaman Kwankwaso sun zo ne bayan kakakin gwamnan Kano, Sanusi Bature, ya zarge shi da taimakawa shirin sake zaɓen Tinubu ta bayan katanga.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Farfesa Segun Aina, a matsayin sabon Shugaban Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Manyan Ma...
21/05/2026

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Farfesa Segun Aina, a matsayin sabon Shugaban Hukumar Shirya Jarabawar Shiga Manyan Makarantu ta Kasa (JAMB), inda zai gaji Farfesa Ishaq Oloyede wanda wa’adin aikin sa zai kare a ranar 31 ga watan Yulin 2026.

Sanarwar nadin na kunshe ne cikin wata takarda da mai bai wa shugaban kasa shawara kan yada labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Alhamis.

A cewar sanarwar, Farfesa Aina kwararre ne a fannin Injiniyancin Kwamfuta a Jami’ar Obafemi Awolowo da ke Ile-Ife, kuma yana da gogewa a bangaren fasahar sadarwa, tsarin gudanar da jarabawar kasa da kuma gyaran cibiyoyi.

Sanarwar ta kara da cewa Farfesan, wanda zai cika shekaru 40 a watan Yuli, ya yi fice a harkar koyarwa da kuma tsarin gudanarwar zamani, tare da kwarewa mai zurfi a fannin inganta tsarin gudanar da cibiyoyin gwamnati.

Ƙungiyar Kwankwasiyya ta yi martani mai zafi kan zargin da gwamnatin Kano ta yi cewa tsohon gwamnan jihar, Sanata Rabiu ...
21/05/2026

Ƙungiyar Kwankwasiyya ta yi martani mai zafi kan zargin da gwamnatin Kano ta yi cewa tsohon gwamnan jihar, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, na yi wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu aiki a ɓoye domin tunkarar zaɓen 2027.

Zargin ya samo asali ne bayan daraktan yaɗa labarai da hulɗa da jama’a na gidan gwamnatin Kano, Sanusi Bature, yabayyana a wata hira da Arise TV cewa duk wasu matakan siyasar Kwankwaso za su iya amfanar da Tinubu a ƙarshe.

A cewar Sanusi Bature:

“Akwai masu yi wa Tinubu aiki a fili, sannan akwai waɗanda ke iya yi masa aiki a bayan fage.”

Ya ƙara da cewa:

“Ina ganin duk abin da Kwankwaso yake yi zai amfani Tinubu a ƙarshe saboda ya taɓa yi masa aiki a zaɓen 2023.”

Sai dai kakakin ƙungiyar Kwankwasiyya, Habeeb Saleh Mohammed, ya musanta zargin, yana mai cewa ana ƙoƙarin ɓata sunan Kwankwaso ne saboda tsoron tasirin sa a siyasa.

A cewarsa:

“Abin da Sanusi Bature da gwamnatin jihar ke yi yanzu ba komai ba ne face yunƙurin ƙirƙirar labarin da su kansu s**a san ba gaskiya ba ne.”

Habeeb ya ce Kwankwaso mutum ne mai bayyana matsayin sa a sarari kuma ba ya shiga siyasar ɓoye boye.

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa wasu masu anfani da tallafin mai da kuma masu cin moriyar canjin kuɗaɗ...
21/05/2026

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya bayyana cewa wasu masu anfani da tallafin mai da kuma masu cin moriyar canjin kuɗaɗen waje na son ganin bayansa bayan matakan da gwamnatinsa ta ɗauka tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023.

Tinubu ya bayyana hakan ne a Lagos yayin taron ƙaddamar da littafin “The NADECO Story” wanda tsohon sakataren ƙungiyar NADECO, Cif Ayo Opadokun, ya wallafa, tare da karrama waɗanda s**a taka rawa a fafutukar dawo da dimokuraɗiyya a Najeriya.

Address

Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when DNN Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Establishment

Send a message to DNN Hausa:

Share