14/02/2022
Fitaccen mai gabatar da shirye-shirye sannan kuma wanda ya kware a wajen shirya fina-finai wanda ya samu lambobin yabo daban-daban, ABOKI, ya ce, za’a fara haska sabon shirin fim dinsa mai suna Mai Martaba a gidajen Kallo daga ranar 10 ga watan Yuni na wannan shekara.
Aboki ya bayyana hakane yayin wani taron manema labarai da aka shirya a nan Kano domin sanar da fara daukar fim din, yana mai cewa za’a haska film din a fadin gidajen cinema dake kasar nan, kuma ana sa ran zai fito a fitacciyar manhajar nan ta Netflix wadda ta kasance dandalin haska fina finai ta duniya.
Da yake zantawa da manema labarai, Aboki ya bayyana cewa fim din wanda za’a haska a garin Daura zai yi nuni da rin salon a al’adun Hausawa da kuma sarauta.
Ya kuma bayyana cewa kashi 99.9 na wadanda suke cikin film din sabbi ne, wanda hakan zai kara inganta fannin musamman a arewacin kasar nan, tare da sauyawa daga kan tunanin da ake masu na shiga aiyukan ta’adanci da fashin daji da kuma yin garkuwa da mutane.
Mai Martaba wani shiri ne na wasan kwaikwayo na KasarJallaba, wanda ake ci gaba da gabatar dashi a gidan Rediyon Arewa, wanda ke ba da labarin wata tsohuwar masarauta da ta taba samun bunkasuwar ciniki a tsakanin kasashen yankin Sahara, sai dai kuma bata yi wani karko ba,a sakamakon rikicin karbar mulki a tsakanin tsatson Agadashawa masu rike da madafun iko , wanda ya kai ga rushewar daular.