Hasken Nigeria News

Hasken Nigeria News am proud for my skills investigative journalist in my country no communication no society be proud for your future

24/04/2022

Innalillahi Wa Inna Ilaihi Raji'un 😭😭😭

Mun Samu labarin rasuwar Alaramma Muhammad Sani Lawal, ya rasu cikin daren nan a yayin da yake jagorantar Sallar Tahajjud cikin Sujada.

Allah muke roko ya jikansa ya gafarta mishi Allahumma Amin 🤲

✍️ Abdulsalam Ibrahim Dogara

10/04/2022

Good morning every one

12/08/2021

Jami'an DSS Sun Dira Gidan Tsohon Gwamnan Adamawa Kan Fatan Korona Ta Kashe Buhari.
Jami'an tsaron farin kaya na DSS sun yi dirar mikiya a gidan tsohon gwamnan jihar Adamawa Muhammad Jibrilla Bindow sun masa tambayoyi kan batun fatan da shugaban jam'iyyar APC ya yi wa Buhari na cutar korona ta kashe shi ahuta.
DSS sun zagaye Bindow don samun tabbacin maganar yiwa Buhari fatan mutuwa da shugaban APC na karamar hukumar Yola ta kudu a jihar ya yi wanda aka tattaro cewar Sanata Muhammad Jibrilla Bindow ya halarci taron koda aka furta maganar.
Hon. Sulaiman Adamu shi ne shugaban jam'iyyar APC na karamar hukumar Yola ta kudu a wajen wani taron masu ruwa da tsaki wanda Sanata Bindow ya halarta ya yi fatan cutar korona ta kashe shugaban kasa Buhari kowa ya huta mataimakin sa Yemi Osinbajo ya hau.
DSS sun bukaci jin gaskiyar maganar daga bakin Sanata Bindow wanda ke wurin koda lamarin ya faru. kuma Bindow ya basu gaskiyar tabbacin maganar ba tareda tsoro ko fargaba ba.
Tuni dai da uwar jam'iyyar APC ta dakatar da shugaban ta na Yola ta kudu jihar Adamawa akan k**a sa da laifin yiwa shugaban kasa fatan cutar korona ta hallaka shi.
Mi Zaku Ce?

12/08/2021

Gwamnati ta fara binciken yadda fuskokin fatara suke a Nijeriya
Ma'aikatar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa ta Tarayya ta bayyana wani safiyo da ta ke yi kan yadda fatara ta ke ta fuskoki daban-daban a ƙasar nan (Multidimensional Poverty Index (MPI) Survey).
Minista Sadiya Umar Farouq ce ta ƙaddamar da safiyon na MPI ta hanyar yanar gizo a ranar Talata.
A lokacin ƙaddamarwar, ministar ta ce Nijeriya ta bi sahun ƙasashe da su ka fara inganta hanyoyin su na yanke shawarar gudanar da shirye-shirye ta hanyar amfani da bayanan da aka samu daga binciken na MPI.
Ta ce, “Kowa ya amince a yi aiki da tsarin MPI ne saboda hanyoyi daban-daban da kuma yarjejeniyoyin ƙasashen duniya da aka yi, ciki har da Muradan Cigaban Ƙarni na Duniya, wato 'Millennium Development Goals' (MDGs), waɗanda an maye gurbin su da Muradan Cigaba Masu Ɗorewa, wato 'Sustainable Development Goals' (SDGs) domin su shafo sassa daban-daban na rashi wanda shi ne ruhin fatara da abubuwa masu alaƙa da ita.
“Saboda haka abin farin ciki ne mu tafi tare da sauran muryoyi masu ƙarfi wajen hasko muhimmancin aiki da masu ruwa da tsaki daban-daban a kan yaƙi da fatara, kawar da yunwa, bada nagartaccen ilimi, matakan yanayin ƙasa da kuma rungumar kowa, waɗanda dukkan su muhimman abubuwa ne wajen shaidar da MPI ke samarwa.”
Sadiya Umar Farouq ta lura da cewa gwamnatin Muhammadu Buhari ta samu nasarar inganta rayuwar sama da mutum miliyan 10 ta hanyar fidda su daga matsananciyar fatara ta hanyar ɗimbin shirye-shiryen gwamnatin, waɗanda su ka haɗa da shirin inganta rayuwa na ƙasa, wato 'National Social Investment Programme' (NSIP), da GEEP, Npower, NHGSFP da wasu da dama.
Ta ce, “Wannan muradin ya na yin la'akari da yawan jama'ar da ƙasar nan ta ke da shi yanzu wanda ya kai kimanin mutum miliyan 200, da kuma buƙatar samar da ingantacciyar shaida don tsara shiri.
“Don haka Ma'aikatar Harkokin Jinƙai, Agaji da Inganta Rayuwa ta Tarayya ta tsaya tsayin daka wajen yin haɗin gwiwa da hukumomin gwamnati daban-daban, d

12/08/2021

Rundunar 'yan sandan farin kaya ta Najeriya, DSS, ta yi wa tsohon gwamnan Adamawa, Jibrilla Bindow tambayoyi kan halartar taron batanci ga Buhari.
An ce Bindow ya kasance a wurin wani taro inda wasu 'yan jam'iyyar APC s**a yi mugun fata ga Shugaba Buhari.

12/08/2021

Ba zan auri Jahilin miji ba, cewar Jaruma Maimuna Muhd wadda anka fi sani da wata Yarinya

12/08/2021

Gwamnonin APC na so jam'iyyar su ta gaggauta kiran taron gangami na ƙasa
------------------
Gwamnonin jam'iyyar APC sun nemi a gudanar da taron gangami na ƙkasa, domin a zaɓar wa jam'iyyar shugabanni, maimakon ci gaba da tafiya a hannun shugaban riƙo, Gwamna

12/08/2021

Wasu kwamandojin Boko Haram da s**a mika wuya ga Sojoji sun nemi afuwar ‘yan Najeriya.
Cikakken bayanin;

12/08/2021

More Boko Haram Insurgents Surrender In Borno, Beg For Forgiveness

01/08/2021

ƳAN AREWA MUNAFUKKAI NE: Kun ji dadi an k**a Nnamdi Kanu da Sunday Igboho amman kuma baku ji dadin k**a Abba Kyari ba~Shehu Sani
Tsohon Sanatan Kaduna Shehu ya caccaki 'yan Arewa da ke jin haushin abin da ake tuhunmawar mataimakin kwamisshinan 'yan sanda na kasa Abba Kyari da aikatawa.
Sanatan ya ce akwai munafurci a cikin zukatan 'yan Arewa, domin an k**a Sunday Igboho da Nnamdi Kanu sun ji dadi amman saboda munafurci ana tuhummawar Abba Kyari sun ji haushi sun dami mutane da surutu.
Shin ya kuke kallon wadannan kalamai na Shehu Sani?

01/08/2021

Sufeto janar na 'yan sandan Najeriya na son a dakatar da Abba Kyari daga aiki

01/08/2021

Yanzu kam jam'iyyar APC a jihar Zamfara ta zama tsintsiya madaurin ki daya
Jiga-jigan jam'iyyar APC a jihar Zamfara sun sulhunta da junan su.
Sanata Kabiru Ibrahim Marafa ya amince da yin tafiya daya da Gwamna Matawalle, biyowa bayan yunkurin maka Gwamnan a kotu domin kalubalantar shi akan bashi shugabancin jam'iyyar APC da uwar jam'iyyar ta yi bayan da ya fice daga jam'iyyar PDP.
A yanzu dai jiga-jigan siyasar wadanda s**a hada da Abdul-aziz Yari,Sanata Kabiru Marafa, Sani Yariman Bakura, Gwamna Matawalles sun amince da su yi tafiya daya.
Shin ya kuke kallon wannan sulhu?
Anya wannan sulhu zai dore kuwa?
Nasara

Address

Dankande
Kaduna

Telephone

+2348061615083

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hasken Nigeria News posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Establishment

Send a message to Hasken Nigeria News:

Share