Jarumai24 TV

Jarumai24 TV Wannan shafine domin samun labarai da dumi-duminsa.

Wallahi nayi tunanin cewa gilashin masu walda ne, ashe gilashin yafi ƙarfin yaro 😁😁Kudinsa $690 dollars, kusan Naira Mil...
19/04/2026

Wallahi nayi tunanin cewa gilashin masu walda ne, ashe gilashin yafi ƙarfin yaro 😁😁

Kudinsa $690 dollars, kusan Naira Miliyan Daya da Dubu Dari Daya kenan fa (₦1,100,000).

Sunan gilashin = GUCCI GG0541S AUTHENTIC Star Oversized Mask.

17/04/2026

Yadda Wasu Al'amura Ke Faruwa a Gidan Soja, Saurara Ku Samu Darasi,,,,,,,,,,,

Shin menene ra'ayinku gameda kalaman Atiku Abubakar?
15/04/2026

Shin menene ra'ayinku gameda kalaman Atiku Abubakar?

03/04/2026
Rundunar Mata ta Sojin Najeriya ta Yi Bikin Ranar Mata ta Duniya da Ziyarar Gidan Marayu, Taron Ilimi da Kuma DinnerRund...
09/03/2026

Rundunar Mata ta Sojin Najeriya ta Yi Bikin Ranar Mata ta Duniya da Ziyarar Gidan Marayu, Taron Ilimi da Kuma Dinner

Rundunar Mata ta Sojin Najeriya (NAWC) ta gudanar da bikin Ranar Mata ta Duniya ta shekarar 2026 ta hanyar ziyarar jin kai zuwa gidan marayu, gudanar da taron ilimi (seminar), da kuma liyafar cin abinci a Abuja.

An gudanar da taron ilimin mai taken “Give to Gain” a dakin taro na Lt Gen Taoreed Lagbaja Auditorium da ke Muhammadu Buhari Cantonment, Giri, Abuja. Taron ya haɗa mata sojoji masu aiki da waɗanda s**a yi ritaya, masana daga fannoni daban-daban da kuma baƙi na musamman domin tattauna rawar da mata ke takawa a fannoni na jagoranci, hidima da ci gaban ƙasa.

A cikin wata sanarwa da Mai Taimakawa Daraktan Hulɗa da Jama’a na Sojin Najeriya (NAWC), Manjo Nsima Essien ta fitar, ta ce wannan bikin wani ɓangare ne na ƙoƙarin rundunar wajen girmama gudummawar mata da kuma ƙarfafa ci gaban su a cikin sojojin Najeriya da ma al’umma baki ɗaya.

Da take gabatar da jawabin buɗe taron, Baƙuwar girmamawa ta musamman, Birgediya Janar SW Aliyu (Rtd), ta yaba wa Sojin Najeriya kan ƙoƙarinsu na inganta jin daɗi da kuma ci gaban sana’ar mata a cikin rundunar. Ta bayyana cewa Ranar Mata ta Duniya wata muhimmiyar dama ce ta nuna girmamawa ga juriyar mata, nasarorin da s**a samu, da kuma muhimmin rawar da suke takawa a rundunar soji da ma cikin al’umma.

Ta kuma ƙarfafa gwiwar mata sojoji da su ci gaba da kasancewa masu himma, ladabi da ƙoƙarin kai wa ga nasara, tare da karya shinge da kuma bayar da gudummawa mai ma’ana ga ci gaban ƙasa.

Taron ya ƙunshi gabatar da muhimman muƙaloli guda biyu daga masana a fannoni daban-daban. Mataimakiyar Kwamandan Narcotics (DCN) Oyutu Precious Obiageli daga Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi (NDLEA) ta gabatar da muƙala kan illolin shaye-shaye a cikin rundunar soji, musamman a tsakanin mata. Ta bayyana shaye-shaye a matsayin babbar barazana ga lafiyar jama’a da tsaro a duniya, tare da jaddada muhimmancin wayar da kai da matakan kariya.

A muƙala ta biyu, Dr Vivian Ogbonna ta tattauna kan yadda za a ƙarfafa jagoranci, hidima da kuma gadon alheri na mata a cikin rundunar soji. Ta nuna ci gaban da mata s**a samu a fannoni daban-daban, tare da jaddada bukatar magance kalubale k**ar ƙarancin wakilci a manyan muk**ai, matsalolin da ke cikin tsarin aiki, da kuma rashin isasshen jagoranci da horo.

Tun da farko a jawabinsa na maraba, Kwamandan Rundunar Mata ta Sojin Najeriya, Birgediya Janar MS Adamu, ya taya mata murnar wannan rana tare da bayyana su a matsayin ginshikin ci gaban al’umma. Ya ce bikin na bana ya kasance na musamman domin ya zo ne a ranar Lahadi, abin da ya ƙara masa armashi.

Ya kuma jaddada cewa gudummawar da mata ke bayarwa wajen bunƙasa ƙasa da tabbatar da zaman lafiya na da matuƙar muhimmanci.

Birgediya Janar Adamu ya kuma nuna matuƙar godiya ga Babban Hafsan Sojin Ƙasa, Laftanar Janar W Shaibu, bisa amincewa da bayar da kuɗaɗe domin gudanar da bikin cikin nasara, inda ya bayyana shi a matsayin shugaba mai kula da daidaito tsakanin maza da mata wanda ke goyon bayan shirye-shiryen inganta jin daɗi da ci gaban mata a cikin sojoji.

A wani ɓangare na ayyukan bikin, Kwamandan NAWC tare da manyan jami’an rundunar da sojoji sun ziyarci Gidan Marayu na ANAWIM da ke Gwagwalada, Abuja, inda s**a kai tallafin kayan agaji musamman kayan abinci domin tallafa wa yaran da ke zaune a gidan.

A lokacin da s**a isa, Sister Augustina Balogun, Babbar Shugabar gidan marayun, ta tarbe su tare da gabatar da sauran ‘yan’uwa mata masu kula da gidan da kuma bayanin tarihin cibiyar. Ta bayyana cewa kalmar “ANAWIM” ta fito ne daga harshen Ibrananci wadda ke nufin “mafi talaucin talakawa”, tana kuma kula da yara marayu da sauran masu rauni a cikin al’umma.

A nasa jawabin, Birgediya Janar Adamu ya nuna godiya bisa damar da aka ba su na ziyartar gidan marayun da kuma kai tallafin, yana mai cewa wannan alheri ya samu ne da taimakon Babban Hafsan Sojin Ƙasa. Ziyarar ta kuma ƙunshi raye-raye da wakoki da yara s**a gabatar domin nishadantar da baƙin.

Hakazalika, Bataliyar Mata ta 2 ta Sojin Najeriya da ke Nkwagu, Abakaliki, Jihar Ebonyi, ita ma ta gudanar da ayyuka na musamman domin bikin Ranar Mata ta Duniya ta 2026, ciki har da shirin duba lafiyar jama’a da sauran ayyuka da s**a haɗa da mata sojoji, wakilai daga 24 Supply and Transport Regiment, 82 Records Office, 72 Provost Regimental Detachment, matan bariki da kuma ‘yan NYSC.

Bikin ya kammala da liyafar cin abinci (dinner) da Kwamandan NAWC ya shirya domin rufe bikin cikin nasara. Daga cikin abubuwan da s**a faru akwai bai wa masu gabatar da muƙaloli da kuma shugabar gidan marayun kyaututtuka, da kuma ɗaukar hotunan haɗin gwiwa a gidan marayu da wajen taron.








Rundunar Matan Soja ta Najeriya Sun Samu Ƙarin Horaswa kan Jagoranci da Haƙƙin Dan AdamRundunar Matan Sojan Nijeriya (NA...
20/02/2026

Rundunar Matan Soja ta Najeriya Sun Samu Ƙarin Horaswa kan Jagoranci da Haƙƙin Dan Adam

Rundunar Matan Sojan Nijeriya (NAWC) ta kammala cikin nasara Taron Kwata na Farko na shekarar 2026, tare da sabunta kudurinta na ƙarfafa ƙwarewa, bin ƙa’idojin ɗabi’a da inganta tasirin ayyukan mata a rundunar.

A cikin wata sanarwa da Mataimakiyar Daraktar Hulɗa da Jama’a ta Rundunar Matan Soja, Manjo Nsima Essien ta fitar, ta bayyana cewa ranar ƙarshe ta taron ta kunshi jerin muhimman laccoci daga manyan hafsoshin soja da ƙwararrun masana, inda aka mayar da hankali kan ɗabi’ar aiki, kare haƙƙin ɗan Adam, haɓaka jagoranci da kuma shigar da batun jinsi a ayyukan soja.

Tsohon Manjo Janar MJ Wambai ya gabatar da lacca mai taken “Operational Ethics, Human Rights, and Professional Conduct.” A cikin gabatarwarsa, ya jaddada muhimmancin ladabi, bin ƙa’idojin hulɗa a fagen aiki da kuma kare haƙƙin ɗan Adam yayin gudanar da ayyukan soja. Ya bayyana cewa jagoranci na gari da kyawawan halaye su ne ginshiƙai na tabbatar da amincewar al’umma da samun nasara mai ɗorewa a ayyukan soja.

Haka kuma, tsohon Birgediya Janar BET Bello ya gabatar da lacca mai taken “Leadership, Career Pathways, and Command Opportunities for Female Personnel.” Ya ƙarfafa mahalarta taron da su dage wajen neman ƙwarewa, su jajirce a ci gaban aikinsu tare da shirya kansu domin ɗaukar manyan nauyin jagoranci a tsarin Sojan Nijeriya. Ya jaddada cewa ƙwarewa, gaskiya da juriyar aiki su ne muhimman siffofin da ake buƙata domin samun nasarar jagoranci.

Haka zalika, Dakta Temilola George ta gabatar da lacca mai taken “From Policy to Practice: Applying Gender Mainstreaming Tools in Military Operations.” Ta bayyana muhimmancin aiwatar da dabarun da s**a yi la’akari da batun jinsi wajen tsarawa da gudanar da ayyukan soja. Ta nuna cewa haɗa hangen nesa na jinsi na taimakawa wajen inganta tasirin aiki, kyakkyawar hulɗa da al’umma da kuma kare masu rauni.

A jawabin rufewa, Kwamandan Rundunar Matan Sojan Nijeriya, Birgediya Janar MS Adamu, ya nuna matuƙar godiyarsa ga duk mahalarta taron bisa jajircewarsu da rawar da s**a taka. Ya bayyana taron a matsayin wani muhimmin dandali da ya haɗa manyan hafsoshin soja da na hukumomin tsaro daban-daban, inda ƙwarewarsu da ladabinsu s**a taka rawa wajen nasarar taron.

Birgediya Janar Adamu ya yaba da haɗin kai da gudummawar mahalarta taron, yana mai cewa ingancin tattaunawa da jajircewar da aka nuna sun nuna ƙudurin NAWC na ƙarfafa haɗin gwiwa, haɓaka ƙwarewa da kuma shirin aiki.

Ya kuma miƙa godiya ta musamman ga kwamitin shirya taron da masu gabatar da laccoci bisa ƙoƙarinsu na tabbatar da an gudanar da taro cikin tsari da tasiri.

Kwamandan ya bayyana kwarin gwiwarsa cewa ilimin da aka samu da haɗin gwiwar da aka ƙarfafa a yayin taron za su taimaka wajen inganta ayyuka da ƙara tasiri a rundunoni da hukumomin da ke aiki tare da NAWC.








Rundunar Mata ta Sojojin Najeriya Ta Fara Taron Kwana Biyar a Hedikwatar Runduna ta 6 Dake Port HarcourtRundunar Mata ta...
18/02/2026

Rundunar Mata ta Sojojin Najeriya Ta Fara Taron Kwana Biyar a Hedikwatar Runduna ta 6 Dake Port Harcourt

Rundunar Mata ta Sojojin Najeriya (NAWC) ta fara taron horaswa na Kwata na Farko na shekarar 2026 a Hedikwatar Runduna ta 6 ta Sojojin Najeriya, da nufin ƙarfafa rawar da jami’an mata ke takawa a yanayin tsaron ƙasa na zamani.

A wata sanarwa da Mataimakiyar Daraktar Hulɗa da Jama’a ta Sojojin Najeriya, Manjo Nsima Essien ta fitar, ta bayyana cewa taron na kwanaki biyar wanda zai gudana daga 16 zuwa 20 ga Fabrairu 2026, yana ɗauke da taken: “Amfani da Jami’an Mata na Sojojin Najeriya a Yanayin Tsaro na Zamani: Rundunar Mata a Mahanga.”

Da yake buɗe taron a madadin Babban Hafsan Sojojin Najeriya (COAS), Babban Kwamandan Runduna ta 6, Manjo Janar EE Emekah, ya jaddada ƙudirin shugabancin Sojojin Najeriya wajen inganta daidaito tsakanin jinsi, ƙwarewa, da ci gaba da horaswa.

Ya bayyana cewa jami’an mata suna taka muhimmiyar rawa wajen tattara bayanan sirri, hulɗa da al’umma, haɗin gwiwar sojoji da fararen hula, da sauran ayyukan tsaro da ke da matuƙar muhimmanci wajen cimma nasarar aiki, musamman a yanayin ayyukan tsaron cikin gida.

A nasa jawabin maraba, Kwamandan Rundunar Mata ta Sojojin Najeriya, Birgediya Janar MS Adamu, ya ce an tsara taron ne domin ƙarfafa ƙwarewa, ƙarfin guiwa da shirin aiki na jami’an mata a dukkan rundunoni.

Birgediya Janar Adamu ya ƙara da cewa yanayin tsaro mai sauyawa na buƙatar ci gaba da horaswa, daidaitawa da kuma fahimtar rawar da mata ke takawa a tsarin ayyukan Sojojin Najeriya. Ya kuma ƙarfafa mahalarta taron da su yi amfani da damar da aka ba su domin inganta ƙwarewarsu da gudunmawar da suke bayarwa a ayyukan tsaron cikin gida.

Daga cikin muhimman abubuwan da aka gabatar a taron akwai laccoci guda uku masu taken: “Rawar Mata a Samun Bayanai Don Gargaɗin Farko,” “Shirin Aikin Jami’an Mata a Ayyukan Tsaron Cikin Gida na Zamani,” da kuma “Haɗin Gwiwar Sojoji da Fararen Hula da Kare Fararen Hula,” waɗanda manyan hafsoshin soja da s**a yi ritaya – Birgediya Janar TJ Kareem, Kanal OI Mosugu da Birgediya Janar BET Bello – s**a gabatar.

Har ila yau, Manjo Janar A Oyebade (Rtd) ya gabatar da muhimmin jawabi inda ya jaddada muhimmancin shugabanci nagari, ladabtarwa da ƙwarewa a matsayin ginshiƙai wajen ƙarfafa Rundunar Mata. Ya kuma ƙarfafa mahalarta da su rungumi gaskiya, aminci da sadaukar da kai wajen gudanar da ayyukansu.

Ana sa ran taron Kwata na Farko 2026 zai ƙara ƙarfafa ƙudirin Sojojin Najeriya na gina runduna mai haɗin kai, ƙwarewa da shirin aiki domin tinkarar ƙalubalen tsaro na ƙasa.

Daga cikin abubuwan da s**a kayatar a taron akwai musayar kyaututtuka da ɗaukar hoton ƙungiya.










Taskforce Ta Yi Babban Kamu a Kasuwar Dangwaro Jihar Kano, Ta Kwace Magungunan Bogi na Naira Biliyan 1.5Kwamitin Taskfor...
13/02/2026

Taskforce Ta Yi Babban Kamu a Kasuwar Dangwaro Jihar Kano, Ta Kwace Magungunan Bogi na Naira Biliyan 1.5

Kwamitin Taskforce na Jihar Kano kan Tashoshin Mota da Sauran Wuraren Jama’a ya mika magungunan haram da aka kwace da kudinsu ya kai kimanin naira biliyan 1.5 ga Hukumar Samar da Magunguna da Kayan Asibiti ta Jihar Kano (DMCSA) domin ajiya cikin tsaro kafin a lalata su.

Yayin mika kayayyakin, Shugaban Kwamitin, Manjo Adamu Abubakar Usman (Rtd), ya bayyana cewa an kwace magungunan ne daga hannun masu sayar da su a Kasuwar Dangwaro. Ya ce kayayyakin sun hada da magungunan bogi, wadanda aka gauraya ba bisa ka’ida ba, na jabu, wadanda s**a kare wa’adinsu, da sauran magunguna masu illa ga lafiyar al’umma.

Manjo Usman ya tabbatar wa al’ummar jihar cewa kwamitin ba zai yi kasa a gwiwa ba wajen kare lafiyar jama’a da tabbatar da bin ka’idojin lafiya. Ya kara da cewa suna aiki kafada da kafada da shugabannin kasuwanni da sauran masu ruwa da tsaki domin gano da kuma kwace irin wadannan magunguna.

“Wannan wata babbar shaida ce cewa tsarin sa ido namu yana aiki yadda ya k**ata, kuma duk wanda ke kokarin jefa lafiyar jama’a cikin hadari ba za a kyale shi ba,” in ji shi, yana mai gargadin ‘yan kasuwa da masu harkar magunguna da su bi dokoki da ka’idoji, tare da kira ga jama’a da su rika sayen magunguna daga wuraren da aka amince da su kawai.

A nasa bangaren, yayin karbar kayayyakin, Darakta-Janar na DMCSA, Pharm. Gali Sule, ya jaddada kudirin Gwamnatin Jihar Kano na ci gaba da kare lafiyar da rayuwar al’ummar jihar.

“Wadannan magunguna masu hatsari ba kawai haramtattun kayayyaki ba ne — barazana ce ta boye. Suna lalata sak**akon magani, suna kara janyo juriya ga magunguna, suna rage amincewar jama’a da tsarin lafiyarmu, kuma a mafi muni, suna janyo asarar rayuka,” in ji shi.

Ya kara da cewa wannan k**a ya zama gargadi ga duk masu safarar magungunan jabu, yana mai cewa DMCSA tare da Kwamitin Taskforce da jami’an tsaro za su ci gaba da bin diddigi, tona asiri da kuma gurfanar da duk masu hannu a rarraba magungunan da ba su da izini.

Darakta-Janar din ya yaba wa Kwamitin Taskforce kan jajircewa da kwarewa, yana mai cewa kokarinsu ya hana faruwar mummunar illa ga iyalai da dama.

Daga cikin magungunan da aka kwace akwai kwali 199 na Benzhexol Hydrochloride BP 5mg, kwali 5 na CINBUL, Levofloxacin 500mg da sauran magunguna daban-daban.

Mika wadannan kayayyaki ya nuna karfin gwiwar Gwamnatin Jihar Kano wajen yaki da magungunan jabu da kuma kare lafiyar jama’a a fadin jihar.




'a

NAWC Ta Ci Gaba Da Ziyara Ta Musamman Don Ƙarfafa Haɗin Kai da NAHFC da NAOWAKwamandan Rundunar Mata ta Sojin Najeriya (...
11/02/2026

NAWC Ta Ci Gaba Da Ziyara Ta Musamman Don Ƙarfafa Haɗin Kai da NAHFC da NAOWA

Kwamandan Rundunar Mata ta Sojin Najeriya (NAWC), Brigediya Janar MS Adamu, a ci gaba da ziyarce-ziyarcen da yake yi domin sanin aiki da mu’amala tun bayan karɓar ragamar jagoranci a ranar 29 Janairu 2026, ya kai ziyarar girmamawa ga Cibiyar Tarihi da Makomar Sojin Najeriya (NAHFC) sannan daga bisani ya ziyarci Ƙungiyar Matan Hafsoshin Sojin Najeriya (NAOWA) a ranar Talata, 10 Fabrairu 2026, a Abuja.

A cikin wata sanarwa da Major Nsima Essien, Mataimakiyar Daraktan Hulɗa da Jama’a ta Rundunar Mata ta Sojin Najeriya, ta fitar, ta bayyana cewa Brigediya Janar Adamu tare da tawagarsa sun samu kyakkyawar tarba daga Manjo Janar TE Gagariga da manyan hafsoshin cibiyar.

A jawabin da ya gabatar, Kwamandan NAWC ya yaba wa Darakta Janar da tawagarsa bisa jajircewarsu wajen adana tarihi da al’adun Sojin Najeriya tare da kiyaye tarihin rundunar. Ya jaddada muhimmancin tarihi da al’ada wajen inganta ƙwarewa, haɗin kai da alfahari a tsakanin jami’ai masu aiki, musamman mata da ke cikin rundunar.

Da yake mayar da martani, Manjo Janar Gagariga ya gode da ziyarar, yana mai cewa irin wannan ziyara na taimakawa wajen koyar da ladabi da bin ƙa’idoji ga ƙananan hafsoshi. Haka kuma ya jaddada muhimmancin bin dokokin Sojin Najeriya kan amfani da kafafen sada zumunta, musamman ga jami’an mata. Ya kuma sake tabbatar da shirye-shiryen NAHFC na yin haɗin gwiwa da NAWC domin inganta wayar da kai kan tarihi, haɓaka shugabanci da ƙarfafa kishin ƙasa, yana mai bayyana cibiyar a matsayin gada tsakanin jiya, yau da gobe na rundunar.

Bayan kammala ziyarar a NAHFC, Kwamandan NAWC ya kai ziyararsa ta farko ta sanin aiki ga Shugabar NAOWA, Hajiya Safiyyah Hassan Shaibu. Manufar ziyarar ita ce ƙarfafa kyakkyawar alaƙa da haɗin kai, musamman a fannoni da s**a shafi harkokin mata, ƙarfafa su da tallafa wa jami’an mata.

Brigediya Janar Adamu ya nuna jin daɗinsa kan yadda NAOWA ke ci gaba da tallafa wa jami’an mata, tare da jaddada muhimmancin haɗin kai tsakanin NAWC da NAOWA domin inganta haɗin kai, ƙara kwarin gwiwa da samar da yanayi mai kyau ga jami’an mata.

A nata ɓangaren, Shugabar NAOWA ta yaba da ziyarar Kwamandan NAWC tare da sake tabbatar da aniyar ƙungiyar na yin aiki tare da NAWC musamman a harkokin jin daɗi da shirye-shiryen ƙarfafa mata.

An kammala ziyarce-ziyarcen biyu da musayar kyaututtuka da ɗaukar hotunan tunawa.










Birgediya Janar Adamu Ya Ziyarci Muhimman Cibiyoyin Sojojin Najeriya Don Fahimtar Aiki a Giri, AbujaKwamandan Rundunar M...
06/02/2026

Birgediya Janar Adamu Ya Ziyarci Muhimman Cibiyoyin Sojojin Najeriya Don Fahimtar Aiki a Giri, Abuja

Kwamandan Rundunar Mata ta Sojojin Najeriya (Nigerian Army Women Command – NAWC), Birgediya Janar Mohammed Sani Adamu, a ranar Talata 4 ga Fabrairu 2026, ya kai ziyarar fahimtar aiki (familiarization tour) zuwa rukuni da sassa daban-daban na Sojojin Najeriya da ke cikin Barikin Muhammadu Buhari, Giri, Abuja.

Manufar ziyarar ita ce domin sanin shugabannin cibiyoyin, karfafa hadin kai, inganta fahimtar juna, da kuma neman goyon baya mai dorewa don bunkasa hadin gwiwa da daidaiton ayyukan sojoji.

A cikin wata sanarwa da Mukaddashin Mataimakiyar Daraktan Rundunar Mata ta Sojojin Najeriya, Major Nsima Essien, ta fitar, ta bayyana cewa Kwamandan NAWC ya ziyarci muhimman cibiyoyi da dama a yayin rangadin. Daga cikin cibiyoyin da aka ziyarta akwai Rundunar Sojojin Sararin Samaniya ta Najeriya (Nigerian Army Space Command), Kamfanin Gonaki da Kiwo na Sojojin Najeriya (Nigerian Army Farms and Ranches Limited), Sashen Kula da Ma’aikata (Department of Personnel Management), da Makarantar Yaki ta Intanet ta Sojojin Najeriya (Nigerian Army Cyber Warfare School), da sauransu.

Birgediya Janar Adamu ya jaddada muhimmancin hadin kai da gina kawance tsakanin cibiyoyi wajen cimma Manufofin Umurnin Babban Hafsan Sojojin Kasa (Chief of Army Staff Command Philosophy) da burikan dabarun Sojojin Najeriya. Ya kuma tabbatar da kudirin NAWC na yin hadin gwiwa da sassan da aka ziyarta a fannoni k**ar kula da ma’aikata, bunkasa kwarewa, da ayyukan tsaro na yanar gizo.

Ya kara da cewa, ziyarar fahimtar aikin an shirya ta ne domin karfafa fahimtar juna, habaka hadin kai, da kuma amfani da kwarewa da kayayyakin aiki na sassan da aka ziyarta wajen inganta ci gaban ma’aikatan NAWC.

Ziyarar ta kara nuna jajircewar Sojojin Najeriya wajen bunkasa aikin hadin gwiwa, kirkire-kirkire, da gina kwarewa a dukkan umarni da rundunoni, bisa daidaituwa da bukatun tsaro na zamani da ayyukan aiki na yanzu.







“Ba Mu Taɓa Ganinsa Da Dukiya Ba” — Mahaifiyar Umar Wanda Ake Zargi Tayi MaganaSabbin bayanai sun bayyana daga iyayen Um...
19/01/2026

“Ba Mu Taɓa Ganinsa Da Dukiya Ba” — Mahaifiyar Umar Wanda Ake Zargi Tayi Magana

Sabbin bayanai sun bayyana daga iyayen Umar Auwalu, wanda ake zargi da jagorantar kisan wata matar aure da ‘ya’yanta a Dorayi Chiranchi, Kano, inda s**a bayyana halin da ɗansu ya kasance a ciki kafin faruwar wannan mummunan lamari, da kuma irin halin da suke ciki bayan bayyana gaskiya.

Mahaifiyar Umar ta bayyana cewa ɗanta yana taimaka mata da kaɗan-kaɗan daga abin da yake samu, tana cewa sau da dama yana bata naira dubu ɗaya ko dari biyar domin a sayi kayan gida k**ar sabulu. Ta ce sana’ar da yake yi ita ce aikin gini, kuma bata taɓa ganinsa da kuɗi masu yawa ba tun kafin faruwar wannan al’amari.

Ta kara da cewa sun shiga tsananin firgici ne bayan jin labarin kisan, amma ta miƙa al’amarinta ga Allah. A cewarta, bayan ta yi alwala ta yi addu’a tana roƙon Allah da cewa idan har Umar na da hannu a cikin lamarin, Allah Ya sanya mata natsuwa da haƙuri. Ta ce duk da cewa daga bisani an tabbatar da cewa yana cikin waɗanda ake zargi, ta samu kanta cikin natsuwa, abin da ta danganta da ikon Allah.

A nasa bangaren, mahaifin Umar ya bayyana cikakken nesanta kansa daga abin da ɗansa ya aikata. Ya ce bai ga amfanin jinkirta shari’a da yawan kai-komo kotu ba, yana kira da a gaggauta yanke hukunci bisa laifin kisan rayuka da aka aikata.

Mahaifin ya kuma bayyana cewa tuni ya barranta kansa da Umar, yana mai cewa abin da ya aikata ya wuce duk wata soyayyar iyaye. Ya kara da tona wasu laifuka da ake zargin Umar da aikatawa a baya, ciki har da kisan ‘yar uwarsa da aka yi mata azaba mai tsanani, da kuma kisan wata ‘yar uwa ta bangaren uba tare da ‘ya’yanta biyu. A cewarsa, tun da Umar ya amsa cewa shi ne ya aikata wadannan laifuka, bai ga wata mafita ba illa a yanke masa hukunci bisa doka.

Lamarin ya jefa iyayen Umar cikin tsananin damuwa da bakin ciki, inda al’umma da dama ke nuna tausayi da juyayi a gare su, suna bayyana su a matsayin mutanen kirki masu kyakkyawar mu’amala a cikin al’umma.

Masu sharhi kan al’amuran zamantakewa sun bayyana cewa wannan lamari ya nuna yadda mutum zai iya aikata mummunan laifi duk da tarbiyya ko kyawawan halayen iyaye, tare da jaddada cewa Allah ba azzalumin bawa ba ne, kuma kowa zai girbi abin da ya shuka.

A halin yanzu, al’umma na ci gaba da yin addu’a ga Allah Madaukakin Sarki da Ya saukar da natsuwa ga iyayen Umar, Ya amintar da su da sauran al’ummar Musulmi, tare da kawo karshen ta’addanci da kisan gilla a cikin kasa.

YANZU-YANZU: Bincike Ya Nuna Dan Uwa Ne Ya Jagoranci Kisan Matar Aure da ‘Ya’yanta a KanoBinciken da rundunar ’yan sanda...
18/01/2026

YANZU-YANZU: Bincike Ya Nuna Dan Uwa Ne Ya Jagoranci Kisan Matar Aure da ‘Ya’yanta a Kano

Binciken da rundunar ’yan sandan Jihar Kano ke ci gaba da gudanarwa kan kisan wata matar aure da ‘ya’yanta a unguwar Dorayi Chiranchi ya nuna sabon bayani mai tayar da hankali, inda aka gano cewa ɗaya daga cikin waɗanda ake zargi da aikata laifin dan uwanta ne na jini.

A cewar rahotanni daga jami’an tsaro, wanda ake zargi mai suna Umar Auwalu na daga cikin mutanen da aka k**a, kuma binciken farko ya tabbatar da cewa yana da dangantakar jini kai tsaye da matar da aka kashe. Wannan sabon bayani ya ƙara zurfafa girman lamarin tare da tayar da tambayoyi kan dalilan da s**a kai ga aikata wannan mummunan kisan.

Rahotanni sun kuma bayyana cewa akwai tsohuwar rigimar gado tsakanin Umar Auwalu da iyalan mijin matar da aka kashe, wadda ake zargin ta daɗe tana rura wutar rashin jituwa a tsakaninsu. Masu bincike na ganin cewa wannan rikici na iya kasancewa ɗaya daga cikin manyan abubuwan da s**a haifar da shirya da aiwatar da kisan gilla.

Rundunar ’yan sanda ta tabbatar da cewa bincike na ci gaba domin gano cikakken rawar da kowanne daga cikin waɗanda ake zargi ya taka, tare da tattara hujjoji masu ƙarfi da za su taimaka wajen gurfanar da su a gaban kotu.

Al’ummar Kano sun bayyana alhini da damuwa kan yadda rigimar cikin gida ta rikide zuwa ta’addanci mai tsanani, suna kuma kira ga hukumomi da su tabbatar an yi adalci, domin ya zama izina ga wasu masu shirin aikata mak**ancin wannan laifi.

Address

No 1, Mogadishu Layout Kaduna
Kaduna

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jarumai24 TV posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Establishment

Send a message to Jarumai24 TV:

Share

//iconSize: [32, 32], //html: '' }) .bindTooltip(name, { //permanent: true, direction: 'bottom', //offset: L.point(12, 25), //opacity: 0.88, interactive: true }) .bindPopup(name); markersLayer.addLayer(marker); } function getMore() { if (gettingMore) { return; } gettingMore = true; var center = map.getCenter(); $.ajax({ url: "/vicinitysearch", data: { lat: center.lat, lng: center.lng, country: "NIGERIA" } }) .done(function(data) { var added = 0; data.forEach(function(loc) { if (!locationIds.includes(loc.id)) { var mapLoc = {id:loc.id,lat:loc.latitude,lng:loc.longitude,title:trunc20(loc.name),popupHtml:loc.popupHtml,urlPath:loc.urlPath,pictureUrl:loc.pictureUrl}; locations.push(mapLoc); locationIds.push(loc.id); map._addMarker(mapLoc); added++; } }); }) .always(function() { gettingMore = false; }); } map._clearMarkers = function() { markersLayer.clearLayers(); } }); }, 4000); });