Kannywood Trendy

Kannywood Trendy Your #1 source for the latest Kannywood news, movie releases, and behind-the-scenes gists from the heart of Northern Nigeria’s vibrant film industry.

Labarai, Gulmammaki, Ance-Kace da Yayi a masanaantar Kannywood dake Arewacin Najeriya. Kukasancedamu🙏!

Bello Muhammad Bello da aka fi sani da General BMB wadda jarumi kuma darakta ne a Kannywood ya kalubalanci dan gwagwarma...
22/05/2026

Bello Muhammad Bello da aka fi sani da General BMB wadda jarumi kuma darakta ne a Kannywood ya kalubalanci dan gwagwarmaya da kishin al’umma Bello Habeeb Galadanci (wato Dan Bello) da ya fito yayi bayani ko sauya fentin wata makarantar da s**a gyara a jihar Kano.

General BMB ya ce kaloluwan fentin da aka yiwa makarantar na da manufar tallata auren jinsi daya ne. Ya ce turawa ne ke amfani da kalar domin talatawa da nuna goyon baya ga masu sabon Allah.

Saidai wallafe-wallafen General BMB din ya tada kura a kafafen sada zumunta da jawo mabanbanta raayoyi.

Wasu na ganin lallai ya zama wajibi a sauya fentin kamar yadda General BMB yace saboda kar a tallata auren jinsi daya.

Wasu kuma na ganin fenti kaloluwa a dakuna da gine ginen makarantun yara babu ai bu aciki saboda ana haka ne domin kara kwadaitar da dalibai zuwa makaranta da karatu saboda.

Menene raayoyinku?

Jarumi kuma darakta a kannywood, Bello Muhammad Bello da aka fi sani da General BMB ya kalubalanci Dan Bello da ya fito ...
22/05/2026

Jarumi kuma darakta a kannywood, Bello Muhammad Bello da aka fi sani da General BMB ya kalubalanci Dan Bello da ya fito yayi bayanin dalilin da yasa s**a yiwa wata makaranta da s**a gyara kaloluwan fentin da bai dace ba.

Yace kaloluwan fenti sunyi kamanni da irin kaloluwan da masu goyon bayan auren jinsi daya a kasashen Turawa.

Bayan wallafi-Saladin General BMBn yayi mutane na cigaba da bayyana raayoyi mabanbanta.

Wasu naganin bai kamata ayi kaloluwan fentin ba kuma ya dace a sake wani.

Wasu kuma na ganin fentin ya dace domin kawatar da wurin karatu zai kara jan hankali da saka shaawar zuwa makaranta wa daliban. Saboda ko da kasashen Turai hakan akeyi kuma ba da manufar tallatawa ko nuna goyon baya ga masu auren jinsi daya ba.

Menene raayoyinku?

19/05/2026

“Zee Diamond, ya kamata ki dinga fitowa kina faɗawa mutane nawa aka samu da kuma nawa ya rage ayi miki aiki. Haka ne kawai zaisa wasu su taimaka miki. Amma ki daina cewa ‘yan kannyood basu yi miki komai ba ko sun kasa taimaka miki. Jinyar ki na bukatar miliyoyi. Kuma ba kowa bane zai iya taimakawa da waɗannan kuɗaɗan.”

Saƙon jaruma Umma Shehu.

Shahararren mawaƙi, Aminu Abubakar Ladan da aka fi sani da Alan Waƙa, ya jaddada goyon bayansa da saƙe zaɓar shugaban Ni...
18/05/2026

Shahararren mawaƙi, Aminu Abubakar Ladan da aka fi sani da Alan Waƙa, ya jaddada goyon bayansa da saƙe zaɓar shugaban Nijeriya, Bola Tinubu, a zaɓukan dake tafe.

Mawaƙin yayi wannan magana ne a wata hira da jaridar online ta DLC Hausa inda ya shaida masu cewa cire tallafin man fetur ma da talakawa ke maganar ana shan wahala asali marigayi tsohon shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari, ne ya assasa tubalin cire wa. Shi Tinubu aiwatarwa yayi.

Alan Waƙa na cikin manya-manyan mawaƙa da jaruman kannywood da Dauda Rarara ke jagoranta a ƙarƙashin wata ƙungiya mai suna “Triple R Kannywood Renewed Hope”, Ƙungiyar da zata wayar da kan ‘yan arewa domin sake zaɓar shugaba Tinubu a karo na biyu.

Menene raayoyinku?

Jarumin Kannywood, Lawan Ahmad, ya sanar da cewa sun kammala taron kwana uku na  ƙungiyar masoya APC a kannywood da ake ...
18/05/2026

Jarumin Kannywood, Lawan Ahmad, ya sanar da cewa sun kammala taron kwana uku na ƙungiyar masoya APC a kannywood da ake kira “Triple R Kannywood Renwed Hope.”

A cewar jarumin shugaban ƙungiyar, mawaƙi Dauda Rarara, ya baiwa kowanne mahalarcin taron somin taɓi na naira dubu 100.

Lawan ɗin yace sun rufe ɗaukar mambobin ƙungiyar tasu da zata fara tallata takarar jam’iyyar APC a duk faɗin Nigeria musamman yankin arewa.

Menene raayoyinku?

18/05/2026

Jarumar kannywood Zee Daimond na cigaba da jinya cikin kunci na rashin kudin jinyar.
Allah ya bata lafiya.

Hukumar Tace Fina-finai ta Kano ta dakatar da jaruman Kannywood Adam Garba da Amina Uba Hassan daga harkokin fim na tsaw...
17/05/2026

Hukumar Tace Fina-finai ta Kano ta dakatar da jaruman Kannywood Adam Garba da Amina Uba Hassan daga harkokin fim na tsawon shekara guda.

Hukumar ta ce ta ɗauki matakin ne bayan wani bidiyo da ta bayyana a matsayin saɓa wa tarbiyya ya haddasa ce-ce-ku-ce a Kano.

A bidiyon wani ɓangare ne na wani fim mai suba “Abadan” da kamfani mai suna RR Production TV ke ɗauka ya mamaye kafafen sada zumunta inda jarumar da jarumin kr zaune kugu da kugu da kuma nuna kamar zasuyi musabaha da juna.

Shugaban hukumar, Alhaji Abba El-Mustapha, ya gargadi masu shirya fina-finai da daraktoci da kada su yi aiki da su yayin dakatarwar, yana mai cewa duk wanda ya karya umarnin zai fuskanci hukunci.

Shin kun goyi bayan wannan hukunci ko kuwa ya yi tsauri?

Tsohuwar Jarumar Kannywood, Ummi Zee Zee, tayi iƙirarin cewa “Da can Ibrahim Badamasi Babangida ya taɓa zama saurayin[t]...
15/05/2026

Tsohuwar Jarumar Kannywood, Ummi Zee Zee, tayi iƙirarin cewa “Da can Ibrahim Badamasi Babangida ya taɓa zama saurayin[t]a, … amma yanzu abokai ne kawai kuma [suna]… mutunta junanmu…”

Jarumar ta ƙara da cewa yanzu tana da saurayi wanda ba ɗan masana’antar fim ba ne, kuma suna shirin yin aure nan gaba kaɗan.

Kalaman nata sun jawo ce-ce-ku-ce da mamaki a kafafen sada zumunta, inda mutane da dama ke ta tofa albarkacin bakinsu kan iƙirarin alaƙar da ta taɓa haɗata da tsohon shugaban ƙasar Najeriya, Janar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB).

Menene raayoyinku?

News credit: Sagacious Bello Lukman/Facebook

Gwamnatin Tarayya ta haramta wa masu digirin girmamawa amfani da lakabin “Dr”, domin dakile yadda ake bai wa mutane wann...
06/05/2026

Gwamnatin Tarayya ta haramta wa masu digirin girmamawa amfani da lakabin “Dr”, domin dakile yadda ake bai wa mutane wannan karramawa ba bisa ƙa’ida ba.

Ministan Ilimi, Tunji Alausa, ya ce an ɗauki matakin ne domin kawo ƙarshen siyasantar da digiri da kuma amfani da shi wajen neman alfarma ko kuɗi.

Matakin ya zo ne bayan ce-ce-ku-ce daga mutanen gari da s**a daga ‘yan boko yadda ake bada digirin girmamawar wa mutanen da basu cancanta ba da kuma zubar da ƙimar kalmar wacce tafi dacewa da ‘yan boko da likitoci.

A baya-bayan nan, bayan bai wa fitaccen mawaƙi Dauda Rarara digirin girmamawa, lamarin ya haddasa ce-ce-ku-ce da s**a daga jama’a da masana, inda ake tambayar cancantar makarantar da kuma ingancin wannan karramawa.

Gwamnati ta kuma gargadi jami’o’i da su bi sabbin ƙa’idoji ko su fuskanci hukunci.

Menene raayoyin ku?

Fitacciyar jarumar Kannywood mai yawan jawo cece-kuce, Fatima Hussaini wacce aka fi sani da Maryam Labarina, ta sake yin...
06/05/2026

Fitacciyar jarumar Kannywood mai yawan jawo cece-kuce, Fatima Hussaini wacce aka fi sani da Maryam Labarina, ta sake yin martani ga masu s**arta a kafafen sada zumunta.

Jarumar mai tasowa ta bayyana a shafinta na Facebook cewa ba ta rayuwa domin faranta wa mutane rai ba, kuma wannan ne dalilin da ya sa ake kiranta da suna iri-iri tare da ɗaukar ta a matsayin mai tayar da ƙura.

Jarumar takara da cewa masu s**a su cigaba da rubutu da keyboards ɗinsu kawai.

Maryam Labarina ta dade tana jawo cece-kuce duk lokacin da ta fito a kafafen yaɗa labarai. A cikin fitowarta ta baya-bayan nan a wani shiri mai suna Gabon Talkshow, ta bayyana cewa ko a gida ba ta yawan magana da Hausa, lamarin da ya sa kakarta ke kiranta da suna “Ba Hausa”.

Haka kuma, a wani lokaci a baya da ta fito a wani podcast da baiyi farin jini ba mai suna “The Glided Circle,” ta yi wasu kalamai masu ƙarfi game da aure da rayuwar iyali, waɗanda mutane da dama s**a bayyana a matsayin masu saɓawa addini da al’adun Arewa ne.

Shin kuna ganin Maryam Labarina tana da gaskiya ne ko kuwa tana son janyo cece-kuce ne da gangan domin adinga maganarta?

Fitaccen jarumin kannywood, Lawan Ahmad, ya tofa albarkacin bakinsa game da wani gajeran faifayen bidiyo da ya karaɗe ka...
05/05/2026

Fitaccen jarumin kannywood, Lawan Ahmad, ya tofa albarkacin bakinsa game da wani gajeran faifayen bidiyo da ya karaɗe kafafen sada zumunta a kwanannan da ake zargin wasu na aikata abin da Allah baya so.

Jarumin ya nanata matsayarsa da ya saba faɗi cewa kallon mutanen banza da ake yiwa jarumai babu adalci a ciki saboda a cikin su akwai mutanen kirki da kuma na banza.

Jarumin ya kammala da du’a’i na neman Allah ya sauwaƙe.

Menene raayoyinku?

Address

Kannywood
Jos

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Kannywood Trendy posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share