21/08/2021
(Hausa duet)
ILIMI
Sulaiman
Da sunan sa sarki a garemu,
Wanda yayyo ilimi a garemu,
Don mu kori jahilcin kammu,
Don mu koyi hulɗa a tsakanimmu,
Sarki mahalicci ga kowa.
Idris
Nai salati ga habibi na,
Manzo mai makka da Madina,
Mujin khadija da maimuna,
Jibrilu yace yi karatu ga kaliƙi na,
To ya zan tsaya dole na zabura kowa.
Sulaiman
Kunsan fa shi Muhammadu,
Shi aka saukar wa da ilmu,
Sannan ya koyar a garemu,
Don mu gyara dukkan rayuwar mu,
Kunji Annabi uba na kowa.
Idris
Yace mu nemi ilmu har sin,
Neman kunga kuwa babu sin,
Dan haka nai Kira ga matasa ku san sin,
Ilmu shine hasken rayuwa har a sin,
Mai ilmi daban yake murya tai babu tsawa.
Sulaiman
Ilimi daɗi da yawa gareshi,
Yana kore jahilci da ƙyashi,
Yana kawo haske ga mai shi,
Ga imani da kore fushi,
Shi ilimi bashi haska wawa.
Idris
Kusan ilimi gishirin rayuwa,
Da shi naga an canza rayuwa,
Ko babu ko sisi ana tsayuwa,
Haba ace baka neman sa'ar wannan rayuwa!
Maza tashi ka nemi ginshi ƙin rayuwa...
Sulaiman
Shi ilimi da kuke ganin sa,
Ba a yin ƙarya da yin sa,
Don bashi ɓuya ga masu yin sa,
In ko kun yo ƙarya da yin sa,
To lalle zaku zamo tiƙewa.
Idris
In Kai karyar za a ƙure ka a can gaba,
In kai kwazo lallai zaka fito sahun gaba,
Zan yi Kira ga ƴan'uwa matasa a nan gaba,
Su dage neman ilmu ba faɗa b***e gaba,
In kabi wannan lallai zaka dacewa.
Sulaiman
Shi ilimi da kuke ganin sa,
In kayo shi ya nuna kansa,
In ka ƙishi ya ɓoye kansa,
Don bashi barin wasa a kansa,
Don haka mu zam masu dagewa.
Idris
Duk da haka mu dage mu neme shi,
Wanda baida sani rayuwar nan sai ai babu shi,
In ko aka ce kai kallon ka babu arashi,
Kamar Sulaiman ya bada himma shi,
Kuzo muyi koyi da irin wannan rayuwa.
Sulaiman
Tabbas Jama'a sai mu farka,
Mu nemi ilimi banda shirka,
Mu kori jahilci har da hauka,
Malam idris shi ma fa yayi girka,
Na neman ilimi har da dagewa.
Idris
A fagen neman sai mun dage,
Mu sa naci sai mun dage,
Ta haka har aka san daage,
Mui aiki tukuru kar muce zamui ɗage,
Wakar na tafiya ta taho karewa.
Sulaiman
Nan zan tsaya da baituka na,
Dana rero babu bajin ta na,
Sai tunatarwa ga abokai na,
Kai har ma dasu ƴan'uwa na,
Har ga ɗauka cin jama'a nawa.
Idris
Mu dage gun neman ilimu,
Matasa a cikin mu akwai imamu,
Baitukan namu kenan cikin jammu,
Sai wata Rana zaku sake jin mu,
Allah yasa kun ƙaru da baitukan nawa.
✍️ Sulaiman Da Idris