15/06/2026
HON. YAKUBU ADAMU PhD: "ZAN CIGABA DA GINA BAUCHI DAGA INDA AKA TSAYA"
Ɗan takarar Gwamnan Jihar Bauchi a ƙarƙashin jam'iyyar APM, Hon. Yakubu Adamu PhD, ya sake bayyana aniyarsa ta ci gaba da dukkan ayyukan alheri da shirye-shiryen raya ƙasa da s**a amfani al'ummar Bauchi, tare da tabbatar da cewa ba za a bari kyawawan ayyukan ci gaba su tsaya a rabin hanya ba.
A cewarsa, ci gaba ba ya da jam'iyya ko yanki, kuma duk wani aiki da ya amfani jama'a ya kamata a ci gaba da shi domin amfanin al'umma.
Ya jaddada cewa idan Allah Ya ba shi damar jagorantar Jihar Bauchi, zai ɗora daga inda aka tsaya tare da ƙara sababbin manufofi da shirye-shiryen da za su bunƙasa tattalin arziki, samar da ayyukan yi ga matasa, ƙarfafa mata da kuma inganta rayuwar al'umma baki ɗaya.
Hon. Yakubu Adamu PhD ya bayyana cewa manufarsa ita ce gina Bauchi mai cike da dama, adalci da ci gaba mai ɗorewa, inda kowane ɗan ƙasa zai ji daɗin romon dimokuraɗiyya ba tare da nuna bambanci ba.
Ya kuma yi kira ga al'ummar jihar da su ci gaba da haɗa kai, su rungumi zaman lafiya da fahimtar juna, domin cigaban Bauchi aiki ne da ya rataya a wuyan kowa.
"Abin da yake da kyau za mu ci gaba da shi, abin da yake buƙatar gyara za mu inganta shi, domin Bauchi ta fi ƙarfin siyasa."
Haɗin Kai...
Ci Gaba...
Sabuwar Bauchi Mai Haska Kowa.