20/12/2025
SANATOCI DA 'YAN MAJALISU SUN ROKI SHUGABAN KASA TINUBU
A yau Maigirma Shugaban Kasa Tinubu ya ziyarci zauren 'yan majalisun tarayyar Nigeria inda ya gabatar da bajet din Kudin Nigeria da za'a a kashe a shekara mai zuwa
Bayan kammala jawabinsa, Shugaban Majalisar Dattawa yayi roko a madadin 'yan majalisu akan umarnin da Tinubu ya bayar na janye jami'an 'yan sanda daga bawa manyan mutane kariya
Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio yace a halin da suke ciki yanzu, wasu 'yan majalisa ba zasu iya zuwa garuruwansu ba saboda babu 'yan sanda da zasu basu kariya daga mahara, sun shiga cikin damuwa da tashin hankali
Shiyasa ya roki Shugaban Kasa Tinubu akan ya sake duba umarnin da ya bayar na janye 'yan sanda daga jikin manyan mutane 'yan siyasa, domin rayuwarsu na cikin hatsari, a cewarsa
Yanzu ya rage wa Shugaban Kasa Tinubu ya amsa rokon 'yan majalisar, ya sa a dawo musu da 'yan sanda ko kuma yaki amincewa su cigaba da dandana halin tsoro da fargaba da talakawan Arewa suke ciki
Allah Ka jikan talakawan Arewa ba don sun mutu ba