04/05/2021
YAN BINDIGA SUNYI BARAZANAR ZASU KASHE DALIBAN JAMI'AR GREENFIELD
YAN BINDIGA SUNYI BARAZANAR ZASU KASHE DALIBAN JAMI'AR GREENFIELD A YAU
Aliyu Samba
Ƴan bindiga da s**a yi garkuwa da daliɓan jami'ar Greenfield fake jihar Kaduna sunyi barazanar cewa zasu kashe ragowar daliban da suke wajensu muddin ba a biya su abinda s**a nema na fansa ba.
A cikin tattaunawa da akai da sashen Hausa na Muryar Amurka (VOA), sani jalingo wanda yace shine shugaban ƴan bindigar yayi gargaɗi ga gwamnatin Kaduna ko iyayen yaran da s**a ƙi biyan kuɗin fansar da ya kai Naira Miliyan ɗari tare da Babur ƙirar Honda, rashin kawo wannan a yau zai jawo su kashe ragowar daliban.
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ƙauyuka da basu gaza 17 ba suke fuskantar sabbin hare hare daga wasu da ake zargin makiyaya ne a jihar Benuwe. An sace ɗaliban Kaduna da adadin su ya kai mutum 22 a ranar 18 ga watan Afrilu lokacin da yan bindigar s**a kewaye makarantar da misalin karfe 8:30 na dare.
Ance sun nemi kudin fansa da yakai Naira Miliyan ɗari takwas da sakin ɗaliban, sun kashe mutum 5 a cikin su yayin da ake ƙoƙarin samun daidaito akan abinda za a biya.
Jalingo yace: "Ɗalibai 17, wadanda s**a haɗa da mata 15 da maza 2 suna hannun sa, ciki har da jikan Marigayi Sarkin Zazzau Alh Shehu Idris, Wanda sunan sa Hamza"
Ya ƙara da cewa, dangin wadanda aka sace ɗin sun biya su Naira Miliyan 55, amma sun karar da kudin wajen ciyar da su.
"Munji cewa gwamnatin Kaduna ta ce baza ta biya kudin fansa ga masu garkuwa dan su sai mak**ai ba, idan ba a kawo miliyan 100 da juma'a Babur ƙirar Honda (Wanda ake cewa Boko Haram) guda 10 ba, za mu kashe ragowar daliban da ke hannun mu" inji Jalingo.
Ya ce sun kashe mutum 5 daga ciki ne dan su tabbatar da cewa Gwamnatin Kaduna da ta tarayya ta gaza.
Jalingo yace shine "Mai neman Abinci ne" a lokacin da aka tambaye shi ko dan ta'adda ne shi. Ya kuma gargaɗi ga hukumomin da suke saka "Tracker" a jikin baburan da suke kawo musu, saboda mutanen sa basa shiga cikin gari, k**a su zai matuƙar wahala.
Ɗaya daga cikin ɗaliban makarantar mai suna Abigail Usman tayi magana a lokacin da akai wannan tattaunawa ta wayar Tarho, tana kira ga gwamnati da iyayen su da su biya kudin dan kada a kashe su.
Mai magana da yawun gwamnan Kaduna Mohammad Jalinge fa kuma kwamashinan tsaro na ciki da al'amuran cikin gida Samuel Aruwan basu amsa kiran da akai musu ba dan a tattauna game da wannan batun.
Haka yunkurin magana da jagororin jami'ar shima ya gagara sak**akon wayar rejistaran makarantar Bashir Muhammad na kashe.