17/06/2026
KOTUN INGILA TA WANKE DIEZANI DAGA ZARGE-ZARGEN RASHAWA
An wanke Tsohuwar Ministar Mai ta Najeriya Diezani Alison-maduke daga dukkanin zarge-zargen cin hanci da rashawa da mahukuntan Burtaniya su ka tuhume ta.
Wannan Kuma shi ne ya kawo karshen daya daga cikin manyan shari'oin kasa da Kasa da a ka sanyawa Ido, Wanda su ka kunshi wani babban jami'in gwamnati Dan Najeriya.
Alkalin wata Kotu da ke Landan ne ya wanke Tsohuwar Ministar Man daga dukkanin tuhume-tuhume shidda da a ke ma ta, da su ka shafi cin hanci da rashawa, da kitsa makarkashiyar aikata cin hanci.
Wannan kuwa ta faru ne biyo bayan tattaunawa ta tsawon makonni, Wanda ya kawo karshen zaman shari'ar na tsawon watanni.
Hukuncin kuma ya wanke Wani Dan kasuwar Mai da a ke tuhumar ta tare da shi, Olatimbo Ayinde da Kuma Dan uwan ta, Doye Agama daga irin wadannan zarge-zargen.