16/05/2026
DOLE KU BIYA HARAJI IDAN KU NA SON CIGABA; SAKON TINUBU GA YAN NAJERIYA
Shugaban Najeriya, Bola Ahmad Tinubu ya ja hankalin Yan Najeriya da su dauki batun biyan haraji a matsayin wani wajibci a matsayin su na yan kasa, don tabbatar da cigaba.
Shugaban na Najeriya ya ce kudaden haraji ginshiki ne na gudanar da ayyukan raya kasa a fannonin kiwon lafiya da ilmi da sauran abubuwan walwala, wanda babu yadda za a yi su samu ba tare da yan kasa na biyan haraji ba.
"Babu mai biyan haraji, amma kowa na hankoron a samu cigaba. Ku na son hanyoyin sufuri ma su kyau da ingantattun asibitoci, amma ba ku son bayar da gudummuwa ta hanyar biyan haraji" in ji shugaban kasar.
Shugaba Tinubu ya ce mutumin da ke biyan haraji shi ne Dan Kasa. Idan mutum bai biyan haraji, kuma ba dauke ma shi biyan a ka yi ba, to ba ya da kishin kasa.