Huda-Huda Update

Huda-Huda Update News, entertainment, adverts and other media content

16/05/2026

A yanzu haka Alhaji Aminu Dahiru (Computer) shi ne Dan Takarar Dan Majalisar Wakilai daga Mazabar Mashi da Dutsi, a karkashin inuwar jam'iyyar PDP.

A cikin wannan hirar da Huda-Huda Update, ya yi matashiya a kan rawar da jam'iyyar PDP ta taka wajen gina rayuwar jama'a.

YAN BOKO HARAM SUN SACE YARAN FIRAMARE 42Yan ta'addan Boko Haram sun kai hari a makarantar firamare da karamar sakandire...
16/05/2026

YAN BOKO HARAM SUN SACE YARAN FIRAMARE 42

Yan ta'addan Boko Haram sun kai hari a makarantar firamare da karamar sakandire ta M***a, da ke yankin karamar hukumar Askira-Uba ta jihar Borno, in da su ka sace yara 42.

Sanata Ali Ndume da ke wakiltar Borno ta Kudu ne ya yi wannan ikirarin, in da ya ce ya samo bayanan hakan ne daga hukumomin makarantar da Kuma shugabannin al'umma na yankin da abun ya faru.

Ndume ya Kuma jajantawa Yan uwa da iyayen yaran da a ka sace din.

A ranar Juma'a ne dai a ka samu rahotannin cewa Yan Boko Haram sun kai hari a makarantar, in da su ka sace yara da ba a san adadin su ba.

Sanata Ndume ya bayyana harin a matsayin abun tashin hankali matuka, kasancewar ya faru ne a daidai lokacin da yaran ke tsaka da daukar darussan su na safe.

16/05/2026

UBAN DUMA MAI DAWAYYA

MACE DAYA TILO DA KE NEMAN TAKARAR MAJALISAR WAKILAI TA SAMU NASARAR ZABEN FITAR DA GWANI A JIHAR KATSINA An bayyana sun...
16/05/2026

MACE DAYA TILO DA KE NEMAN TAKARAR MAJALISAR WAKILAI TA SAMU NASARAR ZABEN FITAR DA GWANI A JIHAR KATSINA

An bayyana sunan Jamila Abdu Mani, mace daya tilo da ke neman takarar majalisar wakilai, a matsayin wadda ta samu nasarar zaben fitar da gwani na jam'iyyar APC a mazabar Mani da Bindawa.

Nasarar zaben kuwa ta fito ne daga bakin shugaban kwamitin shirya zaben fitar da yan takarar mazabar, Malam Shafi'u Audu Duwan, a karamar hukumar Mani.

DOLE KU BIYA HARAJI IDAN KU NA SON CIGABA; SAKON TINUBU GA YAN NAJERIYAShugaban Najeriya, Bola Ahmad Tinubu ya ja hankal...
16/05/2026

DOLE KU BIYA HARAJI IDAN KU NA SON CIGABA; SAKON TINUBU GA YAN NAJERIYA

Shugaban Najeriya, Bola Ahmad Tinubu ya ja hankalin Yan Najeriya da su dauki batun biyan haraji a matsayin wani wajibci a matsayin su na yan kasa, don tabbatar da cigaba.

Shugaban na Najeriya ya ce kudaden haraji ginshiki ne na gudanar da ayyukan raya kasa a fannonin kiwon lafiya da ilmi da sauran abubuwan walwala, wanda babu yadda za a yi su samu ba tare da yan kasa na biyan haraji ba.

"Babu mai biyan haraji, amma kowa na hankoron a samu cigaba. Ku na son hanyoyin sufuri ma su kyau da ingantattun asibitoci, amma ba ku son bayar da gudummuwa ta hanyar biyan haraji" in ji shugaban kasar.

Shugaba Tinubu ya ce mutumin da ke biyan haraji shi ne Dan Kasa. Idan mutum bai biyan haraji, kuma ba dauke ma shi biyan a ka yi ba, to ba ya da kishin kasa.

WEEKENDERS, MAI DAWAYYA NA GAISUWA
16/05/2026

WEEKENDERS, MAI DAWAYYA NA GAISUWA

Enjoy the videos and music that you love, upload original content and share it all with friends, family and the world on YouTube.

SOJOJIN NAJERIYA DA AMURKA SUN KASHE KWAMANDAN ISISRahotannin da su ka bayyana da sanyin safiyar yau Asabat na nuni da c...
16/05/2026

SOJOJIN NAJERIYA DA AMURKA SUN KASHE KWAMANDAN ISIS

Rahotannin da su ka bayyana da sanyin safiyar yau Asabat na nuni da cewa an hallaka Kwamandan Kungiyar ISIS, Abu-Bilal al-Minuki a Najeriya, wanda ya kasance na biyu a jagorancin kungiyar a duniya baki daya.

An hallaka al-Minuki ne dai a yayin wani samamen da sojojin Najeriya su ka kai da hadin gwuiwar sojin Amurka, a bisa tsarin kawancen tsaro tsakanin Najeriya da Amurka.

Shugaban Amurka Donald Trump wanda ya bayyana nasarar da a ka samu a samamen, ya kuma yabawa gwamnatin Najeriya a bisa goyon bayan da ta bayar wajen gudanar da aikin.

Tuni dai fadar shugaban kasar Najeriya ta fito da sanarwar da ke tabbatar da kisan na al-Minuki, a yayin harin hadin gwuiwar da a ka aiwatar.

Hadin Gwuiwar tsaro a tsakanin Najeriya da Amurka ta fara ne dai tun daga lokacin da kasar Amurka ta ayyana Najeriya a matsayin daya daga cikin kasashen da ta ke sanyawa ido a kan sha'anin tsaro.

WACE FATA KU KE YI WA JAM'IYYAR APC?Jam'iyyar APC na tunkarar fitar da sunayen wadanda za su yi ma ta takara
15/05/2026

WACE FATA KU KE YI WA JAM'IYYAR APC?

Jam'iyyar APC na tunkarar fitar da sunayen wadanda za su yi ma ta takara

AN DAURE WATA MACE SHEKARU 20 KAN DAKON MAKAMAIWata kotu a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke hukuncin daurin shekaru...
15/05/2026

AN DAURE WATA MACE SHEKARU 20 KAN DAKON MAKAMAI

Wata kotu a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke hukuncin daurin shekaru 20 a kan wata mata mai suna Halima Halliru Umar a bisa laifukan da ke da nasaba da ta'addanci.

An yankewa Halima Halliru wannan hukunci ne a sabili da samun ta da laifin mallakar harsasan bindiga AK-47 guda 302, da Kuma yunkurin tallafawa aikata ayyukan ta'addanci.

HUKUMAR KARE HAKKIN DAN ADAM TA NAJERIYA TA NEMI SOJOJI SU BAYAR DA BA'ASI KAN ZARGIN MUTUWAR FARAREN HULAHukumar Kare H...
15/05/2026

HUKUMAR KARE HAKKIN DAN ADAM TA NAJERIYA TA NEMI SOJOJI SU BAYAR DA BA'ASI KAN ZARGIN MUTUWAR FARAREN HULA

Hukumar Kare Hakkin Dan Adam ta Najeriya, NHRC ta bukaci rundunar sojin sama da ta fito da bayani a kan zargin yawaitar mutuwar fararen hula a lokacin hare-haren su na baya-bayan nan.

Wannan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Hukumar ta fitar a Abuja.

Dukkanin wannan na faruwa ne a sakamakon rahotannin da kafafen yada labaru su ka fitar a baya-bayan nan, na zargin samun yawan asarar rayukan fararen hula a hare-haren da sojan sama ke Kai wa.

Hukumar ta ce yawan koken da a ke samu na asarar rayukan fararen hula ya zamo wani babban abun nunin damuwa da ya ci karo da Tsare-tsare da dokokin kare Hakkin Dan Adam na duniya.

INNALILLAHI WA INNAILAIHIRRAJIUNTashar "Huda-Huda Update" na mika sakon ta'aziyya ga iyali da Yan uwa da jama'ar yankin ...
15/05/2026

INNALILLAHI WA INNAILAIHIRRAJIUN

Tashar "Huda-Huda Update" na mika sakon ta'aziyya ga iyali da Yan uwa da jama'ar yankin Tsanni baki daya, a bisa rasuwar Alhaji Ibrahim Bishir Tsanni wanda a ka fi sani da suna MC.

Alhaji Ibrahim MC ya taba rike matsayin Kansila a majalisar karamar hukumar Batagarawa.

Allah Ya gafarta ma sa, Ya sa can ta fiye ma shi nan, ameen.

Address

No. 04, Estate Staff Quarters, Hassan Usman Katsina Polytechnic
Katsina
820102

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Huda-Huda Update posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category