25/08/2026
Sanadiyar Shehu Ibrahim Inyass (RTA) Ne Gwamnatin Najeriya Ta Sanya Hutun Maulidi Ya Zamo Doka A Kasa, Bayan Shehu Ya Zo Taya Najeriya Murnar Samun 'Yanci A Shekarar 1960
Bayan Kasar Najeriya ta samu 'yanci daga mulkin Turawa, Shehu Ibrahim Inyass RTA ya kawo ziyara Najeriya ta musamman domin taya murnan samun 'yanci, da Shehu ya gana da Firayim minista na farko, Sir Abubakar Tafawa Balewa, sai Shehu ya bashi shawara cewa tunda kai Musulmi ne, ya kamata ka sanya ranar Maulidi ya zamo ranar hutu a Najeriya domin murnar zagayowar ranar da aka haifi Annabi Muhammadu (SAW), kamar yanda abokin aikin ka Shugaban Kasa wato (Head Of State) Namdi Azikiwe yake hutun Kirsimeti, nan da nan Sir Abubakar Tafawa Balewa ya Aika da bukatar wannan Dokar Majalisa. Bayan Anyi Zafaffiyar Mahawara Daga Karshe dai Majilisa ta Amince da ranar 12 ga watan Rabi’ul Awwal na kowace shekara ya zama ranar hutu, kuma nan ta ke Tafawa Balewa ya sanya Hannu a wannan doka. Wannan shi ne dalilin da yasa duk ranar 12 ga watan Rabi’ul Awwal gwamnati ke bada hutu.
✍️