Hausa Mirror

Hausa Mirror Hausa Mirror zata dinga kawo muku labarai da harshen Hausa da bidiyo na zamani. Zaku Iya Tuntubarmu Ta WhatsApp- 07017233284
(3)

Shugabannin kananan hukumomi Kano ta Kudu sun bayyana cikakken goyon bayansu ga Kabiru Alhassan Rurum, tare da bayyana s...
26/04/2026

Shugabannin kananan hukumomi Kano ta Kudu sun bayyana cikakken goyon bayansu ga Kabiru Alhassan Rurum, tare da bayyana shi a matsayin jagora jajirtacce kuma gogagge da zai iya kawo karshen matsalolin da yankin Kano ta Kudu ke fuskanta.

Wannan na kunshe ne cikin takardar bayan taro da shugabannin s**a fitar bayan kammala ganawarsu da s**a gudanar a daren jiya, karkashin jagorancin shugabar ƙungiyar ALGON ta jihar Kano, Hajiya Sa’adatu “Matar Soja”, wacce ita ce shugabar karamar hukumar Tudun Wada da Doguwa.

A cewar sanarwar, dukkan shugabannin kananan hukumomin sun sanya hannu kan wannan matsaya ne bisa yakinin cewa Rurum na da kwarewa da gogewa a harkokin siyasa, wanda hakan zai taimaka wajen magance kalubalen da s**a addabi yankin Kano ta Kudu.

Sanarwar ta kuma jaddada cewa hadin kan shugabannin kananan hukumomin na nuna cikakken amincewa da shugabancin Rurum, tare da kira ga al’ummar yankin da su mara masa baya domin samun ci gaba mai dorewa.

Ana Cigiyar Dattijo mai suna Malam Usman, amma anfi kiran shi da suna Baffa mai Shekara 70 da ya bata a yayin zuwa Masal...
25/04/2026

Ana Cigiyar Dattijo mai suna Malam Usman, amma anfi kiran shi da suna Baffa mai Shekara 70 da ya bata a yayin zuwa Masallacin Juma'a na Al-Ansar dake mai Dile.

Idan Allah ya sa an ganshi a taimaka a kawo shi mai Dile Dan Maliki, Wajen gidan Man Yahaya layin Makarantar Balanti, ko akira wannan nomba din. 👇👇👇

0703 782 3336
0703 564 0870

“Ba a taɓa jin maganar cin amana daga gare mu ba,”-Yusuf Buhari.Me za ku ce?
25/04/2026

“Ba a taɓa jin maganar cin amana daga gare mu ba,”-Yusuf Buhari.

Me za ku ce?

Daga Ɓangaren Wasanni: Rahotanni sun tabbatar da cewa kungiyar kwallon kafa ta Barcelona a yanzu tana buƙatar maki Biyar...
25/04/2026

Daga Ɓangaren Wasanni: Rahotanni sun tabbatar da cewa kungiyar kwallon kafa ta Barcelona a yanzu tana buƙatar maki Biyar a wasanni Biyar domin ta lashe gasar Sifaniya.

A yanzu haka tazarar maki 11 tsakaninta da kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid.

Ya kuke kallon wannan batu?

Da take bayyana ra'ayinta a shafukan sada zumunta Waheebah Sa'ad tayi kira ga gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf...
25/04/2026

Da take bayyana ra'ayinta a shafukan sada zumunta Waheebah Sa'ad tayi kira ga gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf, ta ya ja hankalin magoya bayansa kan cin zarafin Jagoran Kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ta kuma bayyana cewa haryanzu suna kaunar gwamna Abba

Me za ku ce?

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya kara da cewa tunda s**a koma jam'iyyar APC shugabannin jamʼiyyar sun riƙe mu han...
25/04/2026

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya kara da cewa tunda s**a koma jam'iyyar APC shugabannin jamʼiyyar sun riƙe mu hannu bibiyu.

Me za ku ce?

Tsohon gwamnan jihar Kano Malam Shekarau ya yi kira ga magoya bayansa na koʼina a tallata jamʼiyyar APC.Me za ku ce?
25/04/2026

Tsohon gwamnan jihar Kano Malam Shekarau ya yi kira ga magoya bayansa na koʼina a tallata jamʼiyyar APC.

Me za ku ce?

Yadda Malam Ibrahim Shekarau yayi rijistar katin jam’iyyar APC a mazaɓarsa ta Giginyu.Me Zakuce?
25/04/2026

Yadda Malam Ibrahim Shekarau yayi rijistar katin jam’iyyar APC a mazaɓarsa ta Giginyu.

Me Zakuce?

Rundunar 'yan sandan jihar Kano ta k**a wani matashi mai shekaru 26, Hassan Umar Gwammaja, bisa zargin sace wani ƙaramin...
25/04/2026

Rundunar 'yan sandan jihar Kano ta k**a wani matashi mai shekaru 26, Hassan Umar Gwammaja, bisa zargin sace wani ƙaramin yaro domin neman kuɗin fansa, lamarin da ya tayar da muhawara kan tasirin fina-finai ga al’umma.

A cewar yansanda, an k**a wanda ake zargin ne bayan ya amsa laifin sace yaron a unguwar Gwammaja. Wanda daga bisani aka sako yaron bayan an biya kuɗin fansa Naira miliyan ɗaya.

Yayin tambayoyi, matashin ya danganta aikinsa da matsin tattalin arziki da tarin basuss**a. Ya ce wannan ba halinsa ba ne, kuma shi ne karo na farko da ya aikata irin wannan laifi.

Abin da ya fi daukar hankali shi ne ikirarin da ya yi cewa ya samu wannan tunani ne daga wani shahararren shirin talabijin na Hausa, Gidan Badamasi.

“Na koya daga Gidan Badamasi. Na ga yadda aka sace yaro da wani attajiri a cikin fim, sai na kwaikwaya,” in ji shi.

Malam Ibrahim Shekarau, tsohon Gwamnan Kano ya karɓi katin shiga jamʼiyyar APC.
25/04/2026

Malam Ibrahim Shekarau, tsohon Gwamnan Kano ya karɓi katin shiga jamʼiyyar APC.

Sanata Abdurrahman Kawu Sumaila ya kai ziyarar duba aikin hanyar Wudil zuwa Gaya har zuwa Shuwarin, Jihar Jigawa.
25/04/2026

Sanata Abdurrahman Kawu Sumaila ya kai ziyarar duba aikin hanyar Wudil zuwa Gaya har zuwa Shuwarin, Jihar Jigawa.

Cikin Hotuna: Daga mazabar Giginyu Inda gwamna Abba Kabir Yusif ya raka tsohon gwamnan kano Malam Ibrahim Shekarau domin...
25/04/2026

Cikin Hotuna: Daga mazabar Giginyu Inda gwamna Abba Kabir Yusif ya raka tsohon gwamnan kano Malam Ibrahim Shekarau domin ya karbi katin shaidar zama dan jam’iyyar APC

Address

Kano
700101

Telephone

+2348056667299

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Hausa Mirror posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share