26/04/2026
Shugabannin kananan hukumomi Kano ta Kudu sun bayyana cikakken goyon bayansu ga Kabiru Alhassan Rurum, tare da bayyana shi a matsayin jagora jajirtacce kuma gogagge da zai iya kawo karshen matsalolin da yankin Kano ta Kudu ke fuskanta.
Wannan na kunshe ne cikin takardar bayan taro da shugabannin s**a fitar bayan kammala ganawarsu da s**a gudanar a daren jiya, karkashin jagorancin shugabar ƙungiyar ALGON ta jihar Kano, Hajiya Sa’adatu “Matar Soja”, wacce ita ce shugabar karamar hukumar Tudun Wada da Doguwa.
A cewar sanarwar, dukkan shugabannin kananan hukumomin sun sanya hannu kan wannan matsaya ne bisa yakinin cewa Rurum na da kwarewa da gogewa a harkokin siyasa, wanda hakan zai taimaka wajen magance kalubalen da s**a addabi yankin Kano ta Kudu.
Sanarwar ta kuma jaddada cewa hadin kan shugabannin kananan hukumomin na nuna cikakken amincewa da shugabancin Rurum, tare da kira ga al’ummar yankin da su mara masa baya domin samun ci gaba mai dorewa.