06/08/2026
SANARWAR MANEMA LABARAI
Karamar Hukumar Kumbotso
06/08/2026
“Haƙƙin al’umma ne mu tabbatar musu da tsaron rayukansu da dukiyoyinsu.”
Gamayyar Ƙungiyoyin Matasan Jihar Kano sun kai wa Shugaban Karamar Hukumar Kumbotso ziyara tare da ba shi lambar yabo.
Gamayyar Ƙungiyoyin Matasan Jihar Kano sun kai wannan ziyara ne ƙarƙashin jagorancin Shugaban Kamfanin Danfodio Islamic Health Center da ke Ɗorayi, Malam Abdullahi Idris Ɗanfodio, domin gabatar da ƙudirorinsu da kuma irin ayyukan da suke gudanarwa, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da shugabancin Karamar Hukumar Kumbotso.
A jawabinsa, mai magana da yawun ƙungiyar ya bayyana cewa an kafa ƙungiyar ne domin daƙile yawaitar faɗan daba da kuma ƙwacen waya da ake samu a unguwanni 28 da ke faɗin Jihar Kano, musamman a ƙananan hukumomin Kumbotso, Kano Municipal, Gwale da Ungogo. Ya ƙara da cewa babban manufarsu ita ce yaƙi da faɗan daba da masu aikata ƙwacen waya domin tabbatar da zaman lafiya da tsaron al’umma.
Shi ma Shugaban ƙungiyar, Dr. Abdullahi Idris Ɗanfodio, ya bayyana cewa sun kawo wannan ziyara ne domin ƙarfafa alaƙa da Karamar Hukumar Kumbotso, tare da neman goyon bayanta wajen yaƙi da ayyukan bata-gari da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin.
A nasa jawabin, Shugaban Karamar Hukumar Kumbotso, Hon. Ali Musa Danmaliki Hardworker, ya bayyana matuƙar farin cikinsa da yadda ƙungiyar ke jajircewa wajen gudanar da wannan aiki mai amfani ga al’umma. Ya ce gwamnatin ƙaramar hukumar a shirye take ta ba ƙungiyar dukkan goyon bayan da take buƙata domin a daƙile duk wani nau’in ta’addanci da aikata laifuka, tare da tabbatar da zaman lafiya.
Shugaban ya ƙara da cewa tsaro na daga cikin manyan abubuwan da gwamnatinsa ta sanya a gaba tun daga hawanta mulki. Saboda haka, ya bayyana ƙungiyar a matsayin abokiyar aiki mai muhimmanci wajen tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma.
Ya ce:
“Haƙƙin al’umma ne mu tabbatar musu da tsaron rayukansu da dukiyoyinsu.”
A ƙarshen taron, Gamayyar Ƙungiyoyin Matasan Jihar Kano sun karrama Shugaban Karamar Hukumar Kumbotso da lambar yabo, bisa gudummawar da yake bayarwa musamman a fannin tsaro da tabbatar da zaman lafiya a yankin.
Signed: ✍️
Alawiyya Wada Isah
Information Officer
Kumbotso LG