Unique hausa Novel

Unique hausa Novel Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Unique hausa Novel, Arts and entertainment, Kano, hotoro, Kano.

27/05/2026

KIƊA A RUWA 3

150...
........Dadah ya jima shiru a gaban mirrorn alamar tunani, kafin yabar dakin gaba daya zuwa dakinsa na bincike. Daki ne da ba kowa ke shiga ba, dan haka komai inda ya ajiye abinsa anan yake ganinsa. Zaune ya kai cikin kujera, gaba daya hankalinsa akan sakon Janar yake, sai dai kafin dubawa wata waya ya ciro a drawer din jikin desk din. Kai tsaye ya shiga WhatsApp, cikin inbox din wata number da babu suna ya danna vedio call. Alamar koma waye a tare yake da wayar bugu biyu ya daga.

Kamar yanda Dadan ya bayyana a screen din haka shima wancan ya bayyana. Yana sanye ne cikin kayan mutane ma'abota zaman sahara, dan kansa zuwa fuskarsa nade suke cikin rawani. Kwayoyin idanunsa kawai ake iya gani. Cike da girmamawa ya risina yana gaida Dadah. Ya amsa masa da kai kawai. Da alama ya riga ya saba da haka saboda babu alamun damuwar rashin maganar ta Dadah ko mamaki ya cigaba da fadin.
“Sir! Ya iso da ita tun awa uku da s**a gabata.
Yanzu haka na karasa dasu cikin gidan”.

“A wane hali take?”.

Dadah ya fada a karo na farko.

“Babu wata babbar damuwa a tare da ita, sai dai
sun shaka mata wani abun daya saka ta barci. A
yanda kuma naji yana fada yana da makarins
zai iya sawa ta farka koda yaushe, amma
hanashi dan ina son muyi magana tukunna”.

“Good. Ka tabbatar idan ta farka komai zataci
daga gareka ne. Kada ka yarda ya bata wani abu
matsayin abinda zata ci koda bayan idonka. Dan
tana tare da juna biyu, na tabbatar zai iya yunkurin
rabata da shi koda ita bazai iya cutar da ta ba”.

“Lallai biri yayi k**a da mutum Sir, dan a daren
jiya dama yace na sama masa likita kwarriya
zatai masa wani aiki. Koda na tambayesa dalili
kuma sai yace idan yazo naji”.

Ido Dadah ya dan runtse da furzar da iska zazzafa.
Cikin sake jaddada umarni ya ce, “Ka hadani da
likitar”.

“In sha ALLAHU Sir, ka bani mintina talatin
kacal”.

Kai kawai Dadah ya jinjina masa. Sai kuma ya
katse kiran....

Kamar jira ake ya yanke kiran mahaukacin bugun
da akema kofar dakin ta fara shiga kunnensa.

“Dadah! Dadah! Aunty Nabeeha!...”

Muryar Asma'u ta sake ratsa kunnuwansa. Tsai ya
mike ya nufo kofar, koda ya bude Asma'un ce dai
a birkice. Ya tabbatar babu lafiya, dan yanda take
kuka hankali a tashe ya ishesa amsa.

"Asma'u calm down".

Ya fada a nutse cike da kulawa. Da kyar ta iya
hadìye kukan da take yi, tana jan numfashi da
share hawayenta. Badan ta samu nutsuwar ba ta
sake nuna masa hanyar downstairs tana fadìn,
"Dadah Aunty Nabeeha ce, kazo dan ALLAH karta
aikata, tace kashe kanta zatayi, ta dakko hypo zata
sha.."

Sosai zuciyarsa ta motsa, dan yasan Nabeeha
da rashin hankalinta. Tun kafin su gama sakkowa
yake jiyo kukanta da surutanta masu kaifi da
dukan zuciya kuwa. Ya dan bi falon daya gama
hargitsewa da kallo, kafin ya sauke idanun nasa
kan Nabeeha dake rike da robar Hypo tana kuka
tamkar ranta zai fita. Gefe Hajiya Hasiba ce da
Ismat ke kuka suma da rokonta kan ta ajiye kayan
hannunta, amma tana tabbatar musu ba zata yi
hakan ba, sai ma hango Dadah daya sakata
zaburowa inda yake tana fadìn, "Idan ku bazakugaya min ba ai shi gashi nan sai ya fada min.”

Dan nesa da shi kadan ta tsaya, shi ko ya zuba
mata ido kawai. Cikin karaji da birkicewar fitar
hayyaci ta ce, “Haysam ka fada min da bakinka,
da gaske tsintacciyar yarinyar nan nada cikin
gudan jininka ko karya waccan shegiyar yarinyar
Rayhana ke yi?”.

Shiru babu alamar Dadah zai yi magana, ya kuma
ki daina kallonta.

“Kenan shirunka na nufin haka ne Haysam? Kenan
akwai wata da zaka iya bama GUDAN JININKA ba
ni ba? Haysam kasan yanda nake sonka kuwa?
Haysam kasan irin daci da kuna da radadin da bur ir
da nake dannewa akan aurenka da ita? Miyyasa
bazaka ga jarumtata ba? Miyasa bazaka fahimci
na karbi hakan wa hukuncin kuskurena da kace
na baya ba? Miyasa bazaka gane ina cigaba da
rayuwa ne kawai saboda kasancewar ka a tare
dani ba? Why zan iya mutuwa akan wannan
maganar Haysam. Ina maka irin soyayyar da
ko Mammah bana jin tana yi maka. Ka tambayi
Mammah zata iya mutuwa a kanka kuwa? To
ni zan iya, zan tabbatar maka zan iya kuma
idan har ka tabbatar min ka kwanta da yar
yarinyar nan har ta samu ciki....”

Kai Dadah ya dan girgiza kawai tare da lumshe
idanunsa da budewa. Yanzun ma bashi da alamar
cewa komai, sai ma motsawa yay na yunkurin
barin wajen...

Fahimtar haka ya saka Nabeeha sake fashewa da
kuka, cikin sambatu da rikicewar tunani ta fara
kokarin bude roban Hybo din hannunta da fadin,
“Tafiyarka na nufin amsar da nake nema Haysam
Shike nan kaje, kaje kawai Haysam, kaje...."

Ganin zata kai robar bakinta Hajiya Hasiba ta
zaburo kanta jikin ta na rawa. "Nabeeha ki ajiye
abin nan, ki saurara ni...."

"Momy bazan ajiye ba, ba kuma zan saurari
kowa ba, gara na kashe kaina. Why kashe k
zanyi, dan dana ga wata da cikin Haysa
ba gara na mutu Momy. Dama kin jima
min Haysam da zurl'ar sa ba kaunata suk
shi naga tabbas, tunda har zai iya yima wata ciki
bani ba, shekara nawa Momy? Shekara nawa ina
cikin damuwar rashin haihuwa da rokonsa muje
muga likita amma yaki, shine yanzu za'a ce min
yar cikina nada cikinsa, Momy gara na mutu dajin
wannan mummunar magan....."

Cikin karajin itama Hajiya Hasiba ta jari
numfashinta. "Idan kin kashe kanki a tunanini
waye yaci nasara Nabeeha? Haysam ne da
janginsa. Kalli kiga, dube su kiga yanda suke cikin
dube shi kina magana bashi da lokacin baki amsa,
shin wannan bai isa ki gane abinda k**e shirin yi
bashi bane mafita?." yanda tai maganar da nuna
su Mammah ya saka Ammar zaburowa, amma sai
Mammah ta rike shi tana mai kallon Hajiya Hasiba
ido cikin ido. Cikin nutsuwarta da Dadah ya gada
ta dan girgiza kanta da murmurshin takaici.

"Kada kiyi wannan kuskuren Hajiya Hasiba. Dan
zai iya zama mafi girman abinda zai saka ki dana
sani. Ki sani ba'a gyara barna da barna, kada
kuma kiyi amfani da son zuciyarki wajen yaudarar
ta. Yin hakan a karshe dana sani yake zama
sak**akon, kuma ke zata kalubalanta. Ki gayama
Nabeeha gaskiya, ita haihuwa ta ALLAH ce Shi ke
badawa a lokacin da yaso, ga kuma war de as?).
Dan Nimrah ta samu karuwa da Muhammad basn
ke nufin ya zabeta bane da wannan matsayin bisa
nashi tsarin, ba kuma haka na nufin Nabeeha
bazata taba samu ba itama, UBANGNI ya fimu
sanin abinda ke boye......"

"Ya boye ko kuka boye? Wayama sani ko wa
abun kukai mata dan kada ta haihun da shi
ba kaunarta kuke ba? Idan ma haka ne
kun gama biyana, dan dana hafa zuri'ata
makiyyata gara ace Nabeeha ta mutu bata hainu
ba. Kuma wlhy a wannan karon dole Haysam ya
sakar min yata, idan ba haka ba kotu ce zata raha
mu".

"Hasiba kenan naji ni makiyarki ce yanda kikace

din, sannan har yanzu baki gama sanin wacece
A'isha ba wlhy, amma a wannan gabar zan
tabbatar miki da ainahina. Ni kuma idan har nice
na dauki cikin Muhammad tsawon watanni, nai
wahalar nakudar haihuwarsa, sannan na shayar
da shi da ruwan jikina bazai taba sakin Nabeeha
ba sai dai ki mutu da wannan bakin cikin. Domin
shine burinki da bazai taba cika ba, sai dai ki
cigaba da jiran lokaci. Halayen banza kuwa kada ki
fasa koya mata, kece zata kalubalanta watarana,
amma jinin Nasiru da Abdul-rasheed har abada
ya kullu a karkashin inuwar aure kenan babu
rabuwa. Dan in har kikaga hakan ta faru sai idan
a dalili daya. Ko na mutu, ko Muhammad ya mutu
Nabeeha ta masa takaba. Ko ita ta mutu ya mata.

wanka ya sallaceta..."

"Wlhy baki isa ba A'isha. Idan kina ganin kinci
nasara a baya na saka Nasir bama danki auren
Nabeeha saboda kin masa asiri keda mataccen
mijinki, sannan kin aura masa wata yar iska ni
kuma a yanzu zan tabbatar miki da ni Hasiba KIDA
A RUWA ce."

"Mi zai hana mu zuba ni da ke to Hasiba".

"Haka kika ce? To shike nan mu zuba din, ni kuwa
zan tabbatar miki nima nice na haifi Nab
k**ar yanda k**e ikirarin kin haifi naki da

"Ni da ke dan halak ka fasa".

Mammah ta fada cikin kakkausan lafazi tana
juyawa da nufin barin falon. Daga kafarta kuma
dai-dai da fasa ihun Ismat da Amimah suna kwala
kiran sunan Nabeeha da takai robar Hypo din na
kan bakinta........✍✍

27/05/2026

KIƊA A RUWA 3

149...
........“Shegiya ALLAH yasa ta tafi kenan”.

Rayhana ta faɗa cikin subutar baki.
A tare Nabeeha da Nana s**a kalleta. Sai dai Nabeeha da fahimtarta ta bata saboda ita Rayhana tai addu’ar babu wani jinkiri ta amsa da “Amin, yar iskar yariya hakkina ne ai. Ba shi ɗan son mutuwa yaje wancan karon ya dawo da ita ba, to bari mu ga wannan karon ya za’a kwashe”. Tai kwafa tana wucewa fuuu sashenta. Ɗanta fasa zuwa kitchen din ma, tunda daya dawo bai nema inda take ba ya tafi wani waje shi ga mijin yariya..

“Lafiya kuwa?”.

Cewar Mamawo tana kalllon Nabeeha.
Cikin takaici ta faɗa mata abinda ke faruwa. Ai kafin ma takai karshe ta ɗauki remote tana ƙoƙarin kunna television din ɗakin Nabeeha dan a nan s**a sauka ita da Hajiya Hasiba duk da Nabeeha din bata so haka ba. Sai dai tayi shiru ne kawai saboda Momyn tasu, duk da dai ta saka a ranta zuwa dare ko gobe zata saka Nana ta gyara musu dayan ɗakin baki tunda su Amima nasu ɗakin dama s**a sauka.

Ba Mamawo kadai ba hatta Hajiya Hasiba dake fama da kanta abin ya mata daɗi. Hak**a su Amimah. Ita kanta Ismat duk da tana son taga ta canja a wannan gābar tana jin kishin Nimrah akan yar uwarta. Musamman akan cikin nan da s**a ji tana da shi wanda suketa faman ɓoyewa. Sai dai a yanzu cikin subutar baki Ismat din ta ce, “ALLAH yasa cikin ya zube a wannan rikicin ma...”

Kaf din su babu wanda bai kalleta ba. Musamman Rayhana da har wata yar zabura tai. Dan ita ce ma ta iya ƙarfin halin faɗin, “Ciki! Waye ke da ciki?”.

Ismat data fahimci subutar bakin data nema yi sai ta tabe baki kawai. Ganin kalllon da kowa ke mata kuma ta ce, “Manta kawai”.

“Kamar ya na manta, malama ya zaki fara magana kiyi shiru. Ai gara ki sanar mana wake da cikin?”.

Harara Ismat da ballama Rayhana. “To anki a faɗi dīn, wai Rayhana miyyasa yanzu baki da kunya? Har ni k**e faɗama wani Malama?…”

Baki Rayhana ta murguɗa tana ƙunkuni. Badan Mamawo nason jin gaskiyar cikin nan ba da sai ta shigar ma yarta faɗan, amma da yake akwai abu a ranta sai tai shiru. Ƙarshe ma Rayhana ta ɗan tsawatarmāwa akan bata son raina na gaba a bar maganar mana. Daga nan aka bar zancen, sai dai kowa fa abu na caccakar masa zuciya. Zuwa can Mamawo ta saka Ismat damowa Hajiya Hasiba wai kunu. Tana fita tabi bayanta kitchen dīn. Rayhana na ganin haka ta lallaba tabi bayansu. A kitchen Mamawo ta titsiye Ismat daɗin baki. Itako da abu keta cima rai kwana da kwanaki dama sai ga hawaye, a take ta fara sanarma Mamawo dīn. Nanah na store laɓe tana ji, hak**a...

Tsabar yanda Rayhana ta gama razana da jin batun wannan ciki sai ji kawai s**ai ta fasa ihun kururuwar data saka har Hajiya Hasiba dake a jangwabe ta fito babu shiri. Haka ma su da suke kitchen. A dai-dai kuma lokacin Dadah ke shigowa falon shima. Sai dai babu wanda a cikinsu hankalinsu ya kai kanshi saboda kururuwar ihun kukan da Rayhana ke yi da kirama kanta ta shiga uku ta lalace.

Mamawo ta daka mata tsawa saboda takaicin yanda take yi kuma taki gayama kowa abinda ya sata yin haukan. Cikin rufewar ido Rayhana ta ce, “Ki kyaleni Mama, ki kyaleni dolene nayi kuka. Ina fa jin binda Ismat ta gaya miki wai ciki ne da shegiyar yarinyar can Nimrah. Why babu shegiyar data isa ta haihu da Haysam a cikinsu sai ni. Ni kadai ce nafi dacewa da shi. Na fisu son shi, na fisu so......”

Tuuuuuu kake jin saukar wani gigitaccen mari na bazata akan fuskar Rayhana. Kafin ma kowa ya gama banbance daga ina marin ya fito, Nabeeha da idannunta s**a gama rufewa ta shako wuyan Rayhana da hannayenta bibbiyu. Tashin hankali kenan wanda ba’a saka maka rana. Dan-danan falon fa ya hargitse, sun gagara kwace Rayhana a hannun Nabeeha dan shaka ta mata yar gaske ga halbi tana kai mata a ciki da ƙafa. Gefe kuma tana kuka da faɗin, “Ni Rayhana, ni k**e fadawa kina son mijina! Mijina Haysam fa, Haysam k**e so! Haysam. Sannan ciki a cikin wata na Haysam ba ni ba....”

Kai da ganin yanda take sambatun ga kuka ga duka kasan ta fita a hayyacinta. Maimakon Dadah yayi koda gyaran murya ne su san ya nan sai ya kara gyara ma ts yana kalllon ikon ALLAH. Ai bai san Nabeehar tashi nada ƙarfi har haka ba sai yau. Oh-oh shi kuma tashi baiwar kenan auren mata yan casRale, ba uwargidan ba amaryar ba... Kamar wasa kuma sai faɗa ya nema canja salo, dan kiri da mizu Mamawo ta fara ƙoƙarin ramawa yarta. Itama shake Nabeeban tayi. Kuka Ismat da Amimah suna ƙoƙarin raba su, yayinda Nanah ke musu video a kaikaice. Hajiya Hasiba kuwa hawaye kawai take tana kallonsu. Dan ko maganar tayi ma bajinta zasuyi ba saboda murya tata bata fita da kyau...

Kamar abin kiranye sai ga su Mammah sun dawo. Malam Almu da hankalisa ke a tashe dan duk hayaniyar da ake yana juyowa ba karamin dadi yaji da dawowar su Mammah din ba, sak**akon a tunaninsa ko da Dadah akeyi, duk da yasan abine mai wahalar gaske. Amma tunda ya dawo kuma yana shiga ne ihun da yake ji ya fara fitowa yana tunanin ko shi ke dukan wani tunda shi kansa yanda yaga gayyar kayan da akayo ɗazu da sabbin bakin gidan ya girgiza.

“Mike faruwa a gidan haka?”.

Mammah ta tambayesa hankali tashe.
Kamar abinda Malam Almu ke jira dama kenan. Sai ya fara bayani jiki na rawa. Hankalin Mammah ya tashi, duk da bata jin Muhammad zai saka hannu ya dake su, amma ta sanshi da zuciyar tsiya idan aka kaishi makura. Ai bama tasan ta nufi sashen ba, su Ammar dasu Lailah s**a take mata baya. Dan su duka gidan ne s**a fita aka bar Hanne da yara...

A tare s**ai turus har Mammah ganin Dadah tsaye ga kuma masu dambe a gefe. Ruky ta fara kyalkyalewa da dariya da faɗin, “Ikon ALLAH kaga wani caskale mai daɗin kallo…” bata ƙarasa ba Ammar ya rufe mata baki yana nuna mata Dadah da ido, dan alamu sun nuna bata lura da shi ba ita kam. Tabbacin bata lura dīn ba kuwa idanu ta zazzaro tana komawa baya Ammar ta ɓoye da sauri.

Ja’a’lar danne dariya kawai suke da kyar. Dan ba karamin dadi s**a ji ba ganin Dadah bai hana wannan goge raini ba. Mu’azz kam a waya ya fara dauka a boye dan ya saka a ransa kalllon nan fa bazai wuce Nina ba. ALLAH sarki Mammah da s**a ɗauka makiyar tasu dai ce taje tana musu magana, musamman ma Mamawo dake matsayin babba.

Sai a lokacin Dadah ya motsa. A mamakin su Bilal samansa ya haura abinsa alamar yanzun ma bazai ce komai ba. Ko kuma baya son ma Mammah tace sai yace shiyyasa. Yana ko gama haurawa s**a samu yanda suke so sai bakunan su s**a buɗe....

{{{{{❤️}}}}}

Dadah bai sake bi takan shirmen su Nabeeha ba. Dan abinda ke gabansa yafi ƙarfin wancan haukan. Wanka ya fara gabatarwa, bayan ya fito ya kimtsa cikin kaya marasa nauyi. Yana ƙoƙarin saka turare kiran Janar ya katse shi, wayar ya ɗan zuba ma ido, sai kuma ya ajiye turaren da yake fesawa ya ɗauka.

“Barka da yamma ranka ya daɗe”.

“Haysam ina fatan kana lafiya?”.

Dadah yay ɗan ƙaramin murmushi tamkar yana gaban Janar. Cikin ɗan gyara tsaiwa ya ce, “Alhamdulillah.”

Janar ya ɗan jinjina kai daga can shima. Kafin cikin sauke numfashi ya cigaba da faɗin, “Yanzu wane mataki ka ɗauka?. Dan bai k**ata ace an barta a wajensa ba, duk da yana mahaifinta kodan abinda ke tare da ita.”

A hankali Dadah ya ɗan furzar da iskar bakinsa. Cikin nutsuwarsa da dakewar murya ya bama Janar amsa da:

“Sir! Barin masa ita yafi muhimmanci akan yunkurin amsota tun a yau. Akwai Ibrahim tare da su in sha ALLAHU zai kula da komai.”

“Ka tabbatar babu wani damuwa?”.

“In sha ALLAHU”.

“Shike nan, ALLAH ya ƙara tsare masa ita. Na tura maka sako kai da Imran akan tattaunawar mu da mutumin nan. Shima mai wancan binciken ya tabbatar min ya kammala. Na bashi email ɗinka ya tura sai ka tsumayi sakonsa dan na tabbatar masa bamu da isashen lokaci.”

“Okay Sir. Sannu da ƙokarin”.

“Ku ke da sannu Haysam, dan kune ke aiki da jikinku da lokacinku da ƙwakwalwa har iyalanku na fuskantar haɗari. ALLAH ya cigaba da kare ku”.

“Amin ya rabbi, tare da kai da zuri’armu baki ɗaya”.

Janar yay murmushi mai sauti Dadah na iya jinsa, kafin yay masa sallama ya katse kiran. Dadah ya sauke numfashi mai nauyi yana ajiye wayar, sai kuma ya ɗan zubama kansa ido ta cikin mirror..........✍

27/05/2026

KIDA A RUWA 3

148..
.......Har cikin wajen saloon din ɗakin da aka dauki Nimrah Imran s**a shiga. Kai tsaye Dadah wajen window din yaje ya tsaya yana kalllon yanda aka yanka karfen wajen da karamin injin yanka karfe na hannu. Imran dake dube-dube a cikin ɗakin shima ya karaso inda yake. Cikin dan furza da iska mai nauyi ya ce, “Hummm! Sai yanzu na fahimci abinda kake faɗa akan mutumin nan Zak. Yanzu dan ALLAH banda abinsa daya ɗauketa me zata masa? Ai dai yasan aure ne da ita ko”.

Dadah yay ɗan murmushi k**ar bazaice komai ba. Dan har yanzu idanunsa nakan karfen window din ne, duka hannayensa a cikin aljihun wando, sai kuma ya juyo yana kalllon Imran din. “Yaci darajar haihuwa. Ya tsira da mutuncin sunan MAHAIFI. Abu ɗaya ne idan yay kuskuren aikatawa a wannan gābar zan manta da duk wadan can. Da haka ka gayama Ibrahim da wannan kada son ya kula, dan shine kawai mafitar sa a ɗin abinda zai saka a masa a wannan gābar.”

---

---

“Amma Haysam da yin hakan miyasa bazamu amsota ba a yau? Mutumin nan fa ba wani hankali ne ishe shi ba. Ya riga ya rufe zuciyarsa ruff.”

“Hummm Imran dole ne a barshi da ita a wannan gābar koda na kwana biyu ne. Yin hakan zai bashi damar fitar da abinda ke ransa, ita kuma tasan wanene shi a gareta....”

“Amma miye amfanin hakan? Haysam ciki ne fa a jikin yarinyar nan. Ka kuma tabbatar da yanda baiyi kwari ba razani kawai zai iya zama sanadin komai. Haba dan uwana, bafa komai ake nunama jarumta ba, ba kuma da komai ake tarko ba!”

“Ba tarko na dana masa da ita ba Imran. Kai ma kasan tana da DARAJA, da KIMA, da MATSAYI da bazan ko kwatanta ba. UBANGIJINA shi kadai yasan WACECE ITA a zuciyata, sai dai bani da wata mafita bayan wadda muke kai a yanzu. Duk da a tafin hannunmu yake idan har muka motsa shima zai motsa, kafin hannunmu ya kai gareta shi nashi ya riga namu. Sannan ka sani dole sai tasan wanene shi a gareta idan har muna son sanin sauran SIRRIKAN dake hannunta.”

---

---

“Kenan ba komai Nimrah ta fada mana ba a waccan ranar game da mutanen nan? Ko kana ganin har yanzu bata yarda ba kaine ka kashe mata mahaifiya ba?”

“Hummm Imran kenan, har yanzu baka san waye Nimrah ba. WAYO baiwarta ce. Ko kasan ta hanyar ta kawai zamu iya kaiwa ga BABA cikin sauki.”

“BABA!? Haysam kada ka birkita min tunani dan ALLAH. Taya Nimrah kuma ta fada wannan babbar cakwakiyar? Baba fa kake nagana? Wanda muketa fadi tashi a kwanakin nan saboda kawai musan inda yake kadai. Haba ta yaya ma to?”

Maimakon amsa murmushi Dadah yayi kawai tare da fara taku ya fito a dakin. Dai-dai da isowar IG da kansa. Domin jin alakar wadda aka dauka da NSA da Cheff of staff ya zame masa wajib hakan. Imran baida zabin daya wuce bi yo shi. Sai dai cimmasa ne dai-dai suna gaisawa da IG, gaisuwa ta koma tsakanin manyan uku. Son nuna gwaninta IG ke jaddada su kwantar hankalinsu, a yau din nan Nimrah bazata kwana ba. Dan yanzu haka an sake ninka jami’an tsaron da s**a bi bayan su Mole. Dadah shi dai kalace komai ba, dan bazai hanasu aikinsu ba, amma yasan bazasu iya k**a Mole ba, saboda a yanzu...

---

---

Maimakon amsa murmushi Dadah yayi kawai tare da fara taku ya fito a dakin. Dai-dai da isowar IG da kansa. Domin jin alakar wadda aka dauka da NSA da Cheff of staff ya zame masa wajib hakan. Imran baida zabin daya wuce biyo shi. Sai dai ya cimmasa ne dai-dai suna gaisawa da IG. A take gaisuwa ta koma tsakanin manyan uku. Cikin son nuna gwaninta IG ke jaddada su kwantar da hankalinsu, a yau din nan Nimrah bazata kwana ba. Dan yanzu haka an sake ninka jami’an tsaron da s**a bi bayan su Mole. Dadah shi dai baice komai ba, dan bazai hanasu aikinsu ba, amma yasan bazasu iya k**a Mole ba, saboda a yanzu haka ya samu sako daga yaronsa Ibrahim cewar Mole ya isa da Nimrah bakin gabar da zai tsallaka da ita, dama kuma da saka hannunsu ya samu duk damar, hatta abokin da yake tutiya da shi akan komai yaronsu ne, zama su iya cewa sune suke tsara masa duk abinda yake aikatawar a yanzu, musamman dabarun guduwa da Nimrah. Wannan harbe-harben da mallake yaran Dagger ne kawai ya gama goge musu hadda akai, dan sun barsa da basirarsa anan, ya kuma tabbatar musu shima shege ne ashe, tunda ya goge musu hadda koda basu fada ba...
...Daga nan wajen asibiti s**a nufa duba su T-Dalha da Faro ke tare da su. Sun samu an cire musu harsashin, sai dai T-Dalha na cikin mawuyacin hali daya tada musu hankali. Ba harbin ne kadai kuma ya wajigashi ba harda halin da dan uwansa ke ciki dauke Nimrah. Sam baiyi tunanin bushewar zuciyar tasa har takai hakan ba fa.

Sauran dai alhamdullahi, dan duk barci suke. Sai cikin yaran su Molen da duk da anyi treating dinsuma amma hannayensu da handcuffs an had a da gado. Hak**a Dagger yana asibitin, Handcuffs kuma shi kafa da hannu ma aka saka masa, sannan ‘yan sanda biyar ne a dakin da aka ajiye shi kadai. Da alama shi tashi damar ta goma karewa a yau tunda yazo hannun su Dadah.

---

Maimakon amsa murmushi Dadah yayi kawai tare da fara taku ya fito a dakin. Dai-dai da isowar IG da kansa. Domin jin alakar wadda aka dauka da NSA da Cheff of staff ya zame masa wajib hakan. Imran baida zabin daya wuce biyo shi. Sai dai ya cimmasa ne dai-dai suna gaisawa da IG. A take gaisuwa ta koma tsakanin manyan uku. Cikin son nuna gwaninta IG ke jaddada su kwantar da hankalinsu, a yau din nan Nimrah bazata kwana ba. Dan yanzu haka an sake ninka jami’an tsaron da s**a bi bayan su Mole. Dadah shi dai baice komai ba, dan bazai hanasu aikinsu ba, amma yasan bazasu iya k**a Mole ba, saboda a yanzu haka ya samu sako daga yaronsa Ibrahim cewar Mole ya isa da Nimrah bakin gabar da zai tsallaka da ita, dama kuma da saka hannunsu ya samu duk damar, hatta abokin da yake tutiya da shi akan komai yaronsu ne, zama su iya cewa sune suke tsara masa duk abinda yake aikatawar a yanzu, musamman dabarun guduwa da Nimrah. Wannan harbe-harben da mallake yaran Dagger ne kawai ya gama goge musu hadda akai, dan sun barsa da basirarsa anan, ya kuma tabbatar musu shima shege ne ashe, tunda ya goge musu hadda koda basu fada ba...
...Daga nan wajen asibiti s**a nufa duba su T-Dalha da Faro ke tare da su. Sun samu an cire musu harsashin, sai dai T-Dalha na cikin mawuyacin hali daya tada musu hankali. Ba harbin ne kadai kuma ya wajigashi ba harda halin da dan uwansa ke ciki dauke Nimrah. Sam baiyi tunanin bushewar zuciyar tasa har takai hakan ba fa.

Sauran dai alhamdullahi, dan duk barci suke. Sai cikin yaran su Molen da duk da anyi treating dinsuma amma hannayensu da handcuffs an had a da gado. Hak**a Dagger yana asibitin, Handcuffs kuma shi kafa da hannu ma aka saka masa, sannan ‘yan sanda biyar ne a dakin da aka ajiye shi kadai. Da alama shi tashi damar ta goma karewa a yau tunda yazo hannun su Dadah.

---

---

Sun dan UNIT Z... zaman t... aunawa. Tun a shafin farko da Imran ya fara dubawa na bayanan da Dadah ya bashi ya d**o yana kallonsa. “Bazan iya hakurin kaiwa karshe ba Haysam. Kenan shugaban kasar S.A nada alakar jini da Nimrah ta bangaren UWA?”

Dadah dake kallonsa shima ya jinjina masa kai kawai batare da yace komai ba.

“Tab din! Tirkashi. Yanzu na fahimci damar da Baba ya samu mai yawa na ajiye yara irin su Sulaiman da su Sanda har ana basu horo a can. Amma miyasa bazai buda mana waye Baba ba, tunda ya sanshi, sani irin wanda a kaf bayanan bincikenmu babu wanda yay masa”.

“Yace bazai ci amana ba, sannan bazai karya alkawari ba. Na koma nabi ta hanyar AMANATA zan san BABA cikin sauki, zan kuma san inda yake cikin sauri.”

“Yanzu ya zamuyi da Mammah? Dan na tabbatar hankalinta a tashe yake. Idan kuma har bataga Nimrah ta dawo gabanta ba bazai kwanta ba.”

“Ni kaina ita ce kadai damuwata. Amma kai ya kake ganin za’ayi?”

“Haysam muyi mata bayani kawai, nasan zata fahimce mu.”

“Shike nan hakan za’ayi. Naga yau Janar ya gana da mutumin nan fa. Dan ina shiga government House nake ganin fitarsa. Imran na gaji da ganin mutanen nan haka nan.”

“Bakai kadai ba, amma ka kara hakuri komai ai yaz o karshe. Zuwa gobe in sha ALLAHU zan bada lists din wad an da za’aje har gida a dauka in har basu kawo kansu ba, dan 8am dama muka saka musu matsayin cikar lokaci. Naso da T-Dalha za’ai aikin, ga kuma halin da yake ciki”.

“Karka damu a canja shi da wani, tunda bamu d isashen lokaci. Dan na fahimci sai na zauna na bude masa wani abu ko zamu samu kwanciyar hankalin sa akan dan uwansa.”

“Tsarin yayi. Malamin ka fa ya za’ai da shi? Duk na nasan bashi da tabbacin da saka hannunka a k**ashi”.

Dadah yay murmushi har hakoransa na bayyana. Ba komai ya tuna ba sai Malam Su...

---

“Bakai kadai ba, amma ka kara hakuri komai ai yazo karshe. Zuwa gobe in sha ALLAHU zan bada lists din wad an da za’aje har gida a dauka in har basu kawo kansu ba, dan 8am dama muka saka musu matsayin cikar lokaci. Naso da T-Dalha za’ai aikin, ga kuma halin da yake ciki”.

“Karka damu a canja shi da wani, tunda bamu da isashen lokaci. Dan na fahimci sai na zauna da shi na bude masa wani abu ko zamu samu kwanciyar hankalin sa akan dan uwansa.”

"Tsarin yayi. Malamin ka fa ya za’ai da shi? Duk na nasan bashi da tabbacin da saka hannunka a k**ashi".

Dadah yay murmushi har hakoransa na bayyana. Ba komai ya tuna ba sai Malam Su dinsa a shekarun baya. Lallai ya yarda wannan kasar tasu da ake rainawa cike take da kurayen mutane da s**a san aikin bincike da tsaro fiye da yanda ake zato, sai dai rashin samun dama da power din aikin ke dakile su, wasu su koma yima kasashen waje aikin da basirar tasu, wasu su zama ‘yan ta’adda, wasu su koma masana’antar fina-finai, wasu su koma marubutan dake tsara labaran kawai tamkar a gaske abinda suke tsarawar babu shi. ALLAH dai wad aran shugabanni irin na su da s**a sadda su. To saldawa mana, ai duk shugaban da shi burinsa wawaso akan kudin kasa kawai ya gina kansa da zuriyarsa kadai ai ya gama siya da kasar, shiyyasa yake matukar ganin wahalar mutanen yankinmu da basa gane komai sai ka-ce-na-ce mara amfani da amfanatwa. Abin arziki bai karbi wannan yankin ba. Yay dan karamin siririn tsakin da har Imran na kallonsa. Cike da son tsokanarsa ya ce, “Oh wai tunanin yanda zakayi da Malam Su din kake? Ko kewar diyata ne”.

"Kai dai ka sani"

“Bakai kadai ba, amma ka kara hakuri komai ai yazo karshe. Zuwa gobe in sha ALLAHU zan bada lists din wad an da za’aje har gida a dauka in har basu kawo kansu ba, dan 8am dama muka saka musu matsayin cikar lokaci. Naso da T-Dalha za’ai aikin, ga kuma halin da yake ciki”.

“Karka damu a canja shi da wani, tunda bamu da isashen lokaci. Dan na fahimci sai na zauna da shi na bude masa wani abu ko zamu samu kwanciyar hankalin sa akan dan uwansa.”

"Tsarin yayi. Malamin ka fa ya za’ai da shi? Duk na nasan bashi da tabbacin da saka hannunka a k**ashi".

Dadah yay murmushi har hakoransa na bayyana. Ba komai ya tuna ba sai Malam Su dinsa a shekarun baya. Lallai ya yarda wannan kasar tasu da ake rainawa cike take da kurayen mutane da s**a san aikin bincike da tsaro fiye da yanda ake zato, sai dai rashin samun dama da power din aikin ke dakile su, wasu su koma yima kasashen waje aikin da basirar tasu, wasu su zama ‘yan ta’adda, wasu su koma masana’antar fina-finai, wasu su koma marubutan dake tsara labaran kawai tamkar a gaske abinda suke tsarawar babu shi. ALLAH dai wad aran shugabanni irin na su da s**a sadda su. To saldawa mana, ai duk shugaban da shi burinsa wawaso akan kudin kasa kawai ya gina kansa da zuriyarsa kadai ai ya gama siya da kasar, shiyyasa yake matukar ganin wahalar mutanen yankinmu da basa gane komai sai ka-ce-na-ce mara amfani da amfanatwa. Abin arziki bai karbi wannan yankin ba. Yay dan karamin siririn tsakin da har Imran na kallonsa. Cike da son tsokanarsa ya ce, “Oh wai tunanin yanda zakayi da Malam Su din kake? Ko kewar diyata ne”.

"Kai dai ka sani".

Cewar Dadah na hararsa. Shi ko ya sanya dariya.

“Bazan gana da shi ba har sai mun san wanene Baba”.

“Ban san dalilinka ba, amma ALLAH yasa haka shine mafi alkairi”.

“Amin”.

%•%•%•%•%

Su Mammah nacan abinda ya damesu ya ishe su sai jin dirar motocin su Nabeeha s**ayi, babu wanda ya maida hankalinsa a kansu da farko, saboda tunanin sun dawo ne kawai gida da kannenta. Sai da zasu tafi asibiti duba su Kulu da Dadah ya aiko aka daukesu yi sannan s**aga yanda aketa shiga da akwatina da manyan jakunai na kaya. Mammah dai batai magana ba duk da abin ya bata mamaki. Sai Bilal duk da hakurinsa da rashin yawan saka baki a al’amarin Nabeeha yau shine ya fara tankawa. Sai dai kuma tun kafin abin yay nisa ma Mammah ta dakatar da su da fadin su wuce inda zasu. Badan sun so ba dole s**ai shiru ran kowa a dagule...

Anan kuma sashen Nabeeha din ma ta mance shaf da batun dawowar Dadah din sai da Nanah ke sanar mata ta kammala girkin da ta saka a. Rabon ayi ta fito zataje kitchen din ta gam... karo da abinda ake nunawa a television akan daukar Nimrah har aka haskn Dadah da Imran da...

---

Su Mammah nacan abinda ya damesu ya ishe su sai jin dirar motocin su Nabeeha s**ayi, babu wanda ya maida hankalinsa a kansu da farko, saboda tunanin sun dawo ne kawai gida da kannenta. Sai da zasu tafi asibiti duba su Kulu da Dadah ya aiko aka daukesu yi sannan s**aga yanda aketa shiga da akwatina da manyan jakuna na kaya. Mammah dai batai magana ba duk da abin ya bata mamaki. Sai Bilal duk da hakurinsa da rashin yawan saka baki a al’amarin Nabeeha yau shine ya fara tankawa. Sai dai kuma tun kafin abin yay nisa ma Mammah ta dakatar da su da fadin su wuce inda zasu. Badan sun so ba dole s**ai shiru ran kowa a dagule...

Anan kuma sashen Nabeeha din ma ta mance shaf da batun dawowar Dadah din sai da Nanah ke sanar mata ta kammala girkin da ta saka ta. Rabon ayi ta fito zataje kitchen din ta gani tazo karo da abinda ake nunawa a television akan daukar Nimrah har aka hasko Dadah da Imran da IG. Tsaye tayi ta kasa motsi har Rayhana jata biye bayanta ta iso itama.............✍

---

17/05/2026

147
.........Tunda su Shariffa s**a iso da dukkan abincin da Nimrah ta buƙata jikinta har rawa yake na son a zuba mata taci. Dan babu lallaɓawar da su Aunty Ummi basu mata ba akan tasha ko tea ne amma ta dage akan ita dai tuwon take so. Cikin ikon ALLAH sai gasu sun dawo. Ai da kanta ma ta tashi ta zauna. Idonta a tuwon har Ammie ta gama zubawa. Kafin ma ta gama kawowa bakinta ta kamo cokalin da kanta. Abin nata ma har ya saka Ummu da Mammah murmushi ga tausayi. Su kansu su Mommy sai da ta basu tausayi.
Abin ma bai basu dariya ba sai da tace Ammie ta barta ta saka hannu ita cokalin nan baya ɗibo mata da yawa. Ai a fili yanzu kam kowa yay dariyar. Itako ko'a kwalar rigarta cin tuwon nan take hannun baka hannu ƙwarya. Tas ta cinye tace a ƙara. Ummu tace kodai ta haƙura sai an jima sai ta fara hawaye. Sai kawai ta ɗauka da kanta tama ƙara matan. Kamar wasa nan ma ta fara ci, sai a laumar ƙarshe data rage ta fara yamutsa fuska. Sai kuma ta ture plate ɗin gefe. Idanunta na cika da hawaye tace zata sha ruwa, bata ma gama rufe baki ba sai yunƙurin amai. Ga jiki ba ƙwari ta yunƙura zata sauka ta kasa. Sai Ammie ce ta taimaka mata...

ALLAH sarki Nimrah dole ta baka tausayi. Dan babu wanda jikinsa baiyi sanyi ba ganin yanda ta galabaita. Komai sai da ta amayar harta koma ruwa kawai take amai. Sai da aka kira Doctor. Itace tace a dakata to da bata komai, s**a saka mata ruwa ta sake komawa barci.
Jikin kowa ya sake komawa sanyi ƙalau, musamman Ruky da harda hawayenta na tausayin ƴar uwarta. A haka Biebah da Faro s**a iso asibitin suma. Anan kuma kowa ya fahimci itama ta harbu. Babu jimawa sai ga Kawu Tanimu shima. Anan ne su Aunty Ummi s**a s**a ganshi shima ya ƙara saninsu dan dama yana jin sunan su a bakin Kulu. Ga kuma labarin kowa da Nimrah ta sake bashi a weekend ɗin da tai musu. Hajja ma ta iso da kwaɗon ramar da Nimrah tace. Suko su Bilal sai da s**a taso aiki s**a sake zuwa. A lokacin ta farka tayi sallar azhar da la'asar.
Kasancewar kowa ya wuce gida Mammah da kanta ta bata kwaɗon ramar nan wajen ƙarfe biyar. Cikin ikon ALLAH kuma sai gashi batayi aman ba. A lokacin ne Gwaggo Khadijah ta kira dan sake jin yaya jikinta. Sai kuma ga Gwaggo Alawiyya itama. A addu'ar da take jera mata na ALLAH ya inganta ya sauketa lafiya yasa ta tsargu. Mammah na shiga bayi ta tambayi Ruky da Mu'azz da s**a rage basu wuce ba mi likita yace yana damunta.
Nan take s**a gumtsa mata. Nimrah aka shiga zare idon mamaki. Su ko su Ruky suna dariya da tsokanarta. Mammah na fitowa sai taji wata matsananciyar kunya da bata taɓa jin irinta ba zagaye da ita. Tun Mammah bata fahimta ba harta gane. Ita sai abin ma ya bata dariya.
Ita dai Madam Nimrah yanzu baki yayi kurum, taƙi bari su sake haɗa ido da Mammah. Wata irin kunya take ji da mamaki. Wai itace da ciki, cikin ma na haihuwa. Tab ɗin babbar magana. Dama haka ake cikin ashe babu wani wahala? Tunda ita dai bazatace tana jin wani abu ba sai a cikin satin nan koma tace kwana biyar ɗin nan. Haba shiyyasa taga fuskar kowa farin ciki ya kasa ɓoyuwa. To ko Dadah ya sani shima?. Rashin mai bata amsa yasa har barci yay gaba da ita. Dan har Uncle Ammar ya dawo ya ɗauki Ruky da Mu'azz daya biyosu ma bata sani ba...

....★★★....

Duk wannan bidiri da ake yi fa Nabeeha bata ko sani ba. Suna can ma su cikin tashin hankalin rikicewar jikin Momynsu da First Lady ta bari cikin tashin hankali. Lokacin da s**a iso gidan ita da Jiddah al'amarin yaso ɓaci, haka s**a kwasheta zuwa asibiti. Cikin ikon ALLAH kuma nan asibitin da aka kwantar da Nimrah s**a zo. Sai dai kasancewar kowa da sashen da yake babu wanda yasan da zaman ɗan uwansa. Kuma har dare su Nabeeha ɗin na nan. Sai kusan ɗaya saura ta koma gida yau ma. Badan ma Dadah yace mata a daren zasu dawo ba da bazata dawo ba can zata kwana....


{{{{{{×}}}}}}

Su Dadah kam basu sami damar tahowa ba a wannan daren k**ar yanda s**a so. Dan akwai wani aiki da s**a saka ai musu wanda mai kawo musu bayanan bai kai ga kawowa ba sai yau da safe. Dole sai kusan sha ɗaya s**a taho. Abinka da jirgi sha biyu a gida tai musu. Faro da kansa yaje ya ɗakkosu a airport. Tun a hanya zance ke tsikararsa Imran daya fahimta ya kwaɓesa, tare da masa inkiyar yay shiru. Dole Faro ya gimtse.
Dadah dake lure da su sai yasha jinin jikinsa. Amma bai ce komai ba sai da yaga sun ɗauki hanyar daba ta gida ba yay magana. Daddy Imran yace masa karya damu yanzu zai gani. Bakinsa ya ɗan taɓe kawai da girgiza kai ya cigaba da harkokinsa har s**a iso. Cikin ikon ALLAH suna kammala parking sai ga su Kulu da ma na isowa suma. Dan Nimrah ce tace zataci wainar fulawa shine s**a je s**a yo mata.
Cikin girmamawa s**a gaishe su, Imran da Faro s**a amsa, Dadah da yaji k**ar tashin hankali na neman ziyartar zuciyarsa kam ya gagara cewa komai. Sai ma ji da yayi ya ƙagara su shiga ciki. Koda s**a shigan s**a iske duk su Shariffa da su Aunty Mommy da yau ma duk s**a zo asibitin ga su Faro na tambayar mai jiki sai zuciyarsa ta shiga tsitstsinkewa, ɗan sassaucin ma da yaji ganin farin ciki a fuskokin ƙannen nasa da duk s**a iso gare su suna musu sannu da zuwa. Lailah da Shariffa ne kawai kawunansu a ƙasa na girmamawa.
“Mi kuke yi anan?”.
Ya faɗa a maimaikon amsa gaisuwar da suke masa. Caraf Mimi zata fara bayani Imran yay mata alamar tai shiru, sai kuma ya maida duban nasa ga Dadan ya ce, “Mu shiga mana”.
Komai Dadah baice ba ya saka kai cikin ɗakin. Mammah ce kawai sai Doctor data gama duba jikin Nimrah ta zauna suna magana da Mammah akan ciwon kan da Nimrah ɗin ke complain da ciwon jiki. Dan jiya da daddare da ƙyar tai barci tanata musu kuka saboda amai daya takura mata gabannin asuba. Badan hakan ba ma da yau an sallamesu tun sassafe. Amma sai doctor tace a barta zuwa ko gobe ne, dan amai da take yi na galabaitar da ita, kuma bata fasa cewa tana son cin kaza da kaza, idan kuma tacin yaƙi zama saita ƙare da drip.
Yanzu ɗin ma Koko data dage sai tasha ne akaje aka damo mata da safen nan sai amai. Dole aka saka mata drip ɗin, tana kuma farkowa tace wainar fulawa. An kawo wainar kuma barci ya ɗauketa.
Akan Nimrah dake kwance idanun Dadah s**a fara sauka. Sai yaga ta masa wani irin haske fuuu k**ar ba ita ba, ta kuma rame masa a ido alamar bata da lafiya. Duk da zuciyar ƴan maza ta girgiza bazaka gane hakan a cikin idanunsa ba ballema fuska. Sai ma sake kame kansa da yay a nutse ya ƙaraso ciki inda Mammah da Doctor dake faman musu sannu da zuwa suke. Su Faro ne s**a amsa mata, shi ko k**ar ma baiji ba.
Bayan sun gaisa da Mammah da tambayar mai jiki ta amsa musu da kulawa da faɗin Alhamdullah s**a gaisa da Doctor itama. Cike da tsokana Doctor data riga tasan Imran kusan ma a dalilinsa tasan su Mammah dan akwai zumunci a tsakaninsu ta ce ma Daddy Imran ɗin, “Dama kai nake jira ka dawo ai Baban Baby, ka tafa min tukuycina mai tsoka”.
Fuskar Daddy Imran da murmushi ya ce, “In dai tukuyci ne karki damu Doctor. Dan kin cancanci a baki. Ke sai ma kin zaɓa ai”.
“Kai kai to Masha ALLAH. Ko iya haka an biyani ai. ALLAH dai ya inganta mana ya sauketa lafiya.”
A tare Mammah da su Faro s**a amsa da Amin. Yayinda Dadah ke kallonsu kallo irin na tambaya. Amma sai Mammah tayi k**ar ma bata lura da shi ba ta miƙe s**a fice tare da Doctor. Dadah ya sake binta da kallo dan wlhy zuciyarsa bugu take a ƙirjinsa tamkar zata faso waje, idan da ya fahimci maganar doctor na nufin.... Ya kasa ƙarasa tunanin ya zubama Imran da Faro idanu. Su dukansu murmushi suke masa, kafin Daddy Imran da ya matsa a side drawer ɗin gadon asibitin da Nimrah ke kwance ya ɗauki file. Batare da yayi magana ba ya miƙama Dadahn.
Kamar bazai amsa ba sai kuma ya amsa ɗin, tun a takardar farko yaci karo da amsoshin tambayoyinsa. A take tsitstsinkewar zuciyarsa ta ƙaru. Ya ɗago yana kallon Daddy Imran. Shima dake kallon nasa sai ya sakar masa murmushi da jinjina kansa idanunsa na cika da ƙwalla.........✍️

Address

Kano, Hotoro
Kano

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Unique hausa Novel posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share