27/05/2026
KIƊA A RUWA 3
150...
........Dadah ya jima shiru a gaban mirrorn alamar tunani, kafin yabar dakin gaba daya zuwa dakinsa na bincike. Daki ne da ba kowa ke shiga ba, dan haka komai inda ya ajiye abinsa anan yake ganinsa. Zaune ya kai cikin kujera, gaba daya hankalinsa akan sakon Janar yake, sai dai kafin dubawa wata waya ya ciro a drawer din jikin desk din. Kai tsaye ya shiga WhatsApp, cikin inbox din wata number da babu suna ya danna vedio call. Alamar koma waye a tare yake da wayar bugu biyu ya daga.
Kamar yanda Dadan ya bayyana a screen din haka shima wancan ya bayyana. Yana sanye ne cikin kayan mutane ma'abota zaman sahara, dan kansa zuwa fuskarsa nade suke cikin rawani. Kwayoyin idanunsa kawai ake iya gani. Cike da girmamawa ya risina yana gaida Dadah. Ya amsa masa da kai kawai. Da alama ya riga ya saba da haka saboda babu alamun damuwar rashin maganar ta Dadah ko mamaki ya cigaba da fadin.
“Sir! Ya iso da ita tun awa uku da s**a gabata.
Yanzu haka na karasa dasu cikin gidan”.
“A wane hali take?”.
Dadah ya fada a karo na farko.
“Babu wata babbar damuwa a tare da ita, sai dai
sun shaka mata wani abun daya saka ta barci. A
yanda kuma naji yana fada yana da makarins
zai iya sawa ta farka koda yaushe, amma
hanashi dan ina son muyi magana tukunna”.
“Good. Ka tabbatar idan ta farka komai zataci
daga gareka ne. Kada ka yarda ya bata wani abu
matsayin abinda zata ci koda bayan idonka. Dan
tana tare da juna biyu, na tabbatar zai iya yunkurin
rabata da shi koda ita bazai iya cutar da ta ba”.
“Lallai biri yayi k**a da mutum Sir, dan a daren
jiya dama yace na sama masa likita kwarriya
zatai masa wani aiki. Koda na tambayesa dalili
kuma sai yace idan yazo naji”.
Ido Dadah ya dan runtse da furzar da iska zazzafa.
Cikin sake jaddada umarni ya ce, “Ka hadani da
likitar”.
“In sha ALLAHU Sir, ka bani mintina talatin
kacal”.
Kai kawai Dadah ya jinjina masa. Sai kuma ya
katse kiran....
Kamar jira ake ya yanke kiran mahaukacin bugun
da akema kofar dakin ta fara shiga kunnensa.
“Dadah! Dadah! Aunty Nabeeha!...”
Muryar Asma'u ta sake ratsa kunnuwansa. Tsai ya
mike ya nufo kofar, koda ya bude Asma'un ce dai
a birkice. Ya tabbatar babu lafiya, dan yanda take
kuka hankali a tashe ya ishesa amsa.
"Asma'u calm down".
Ya fada a nutse cike da kulawa. Da kyar ta iya
hadìye kukan da take yi, tana jan numfashi da
share hawayenta. Badan ta samu nutsuwar ba ta
sake nuna masa hanyar downstairs tana fadìn,
"Dadah Aunty Nabeeha ce, kazo dan ALLAH karta
aikata, tace kashe kanta zatayi, ta dakko hypo zata
sha.."
Sosai zuciyarsa ta motsa, dan yasan Nabeeha
da rashin hankalinta. Tun kafin su gama sakkowa
yake jiyo kukanta da surutanta masu kaifi da
dukan zuciya kuwa. Ya dan bi falon daya gama
hargitsewa da kallo, kafin ya sauke idanun nasa
kan Nabeeha dake rike da robar Hypo tana kuka
tamkar ranta zai fita. Gefe Hajiya Hasiba ce da
Ismat ke kuka suma da rokonta kan ta ajiye kayan
hannunta, amma tana tabbatar musu ba zata yi
hakan ba, sai ma hango Dadah daya sakata
zaburowa inda yake tana fadìn, "Idan ku bazakugaya min ba ai shi gashi nan sai ya fada min.”
Dan nesa da shi kadan ta tsaya, shi ko ya zuba
mata ido kawai. Cikin karaji da birkicewar fitar
hayyaci ta ce, “Haysam ka fada min da bakinka,
da gaske tsintacciyar yarinyar nan nada cikin
gudan jininka ko karya waccan shegiyar yarinyar
Rayhana ke yi?”.
Shiru babu alamar Dadah zai yi magana, ya kuma
ki daina kallonta.
“Kenan shirunka na nufin haka ne Haysam? Kenan
akwai wata da zaka iya bama GUDAN JININKA ba
ni ba? Haysam kasan yanda nake sonka kuwa?
Haysam kasan irin daci da kuna da radadin da bur ir
da nake dannewa akan aurenka da ita? Miyyasa
bazaka ga jarumtata ba? Miyasa bazaka fahimci
na karbi hakan wa hukuncin kuskurena da kace
na baya ba? Miyasa bazaka gane ina cigaba da
rayuwa ne kawai saboda kasancewar ka a tare
dani ba? Why zan iya mutuwa akan wannan
maganar Haysam. Ina maka irin soyayyar da
ko Mammah bana jin tana yi maka. Ka tambayi
Mammah zata iya mutuwa a kanka kuwa? To
ni zan iya, zan tabbatar maka zan iya kuma
idan har ka tabbatar min ka kwanta da yar
yarinyar nan har ta samu ciki....”
Kai Dadah ya dan girgiza kawai tare da lumshe
idanunsa da budewa. Yanzun ma bashi da alamar
cewa komai, sai ma motsawa yay na yunkurin
barin wajen...
Fahimtar haka ya saka Nabeeha sake fashewa da
kuka, cikin sambatu da rikicewar tunani ta fara
kokarin bude roban Hybo din hannunta da fadin,
“Tafiyarka na nufin amsar da nake nema Haysam
Shike nan kaje, kaje kawai Haysam, kaje...."
Ganin zata kai robar bakinta Hajiya Hasiba ta
zaburo kanta jikin ta na rawa. "Nabeeha ki ajiye
abin nan, ki saurara ni...."
"Momy bazan ajiye ba, ba kuma zan saurari
kowa ba, gara na kashe kaina. Why kashe k
zanyi, dan dana ga wata da cikin Haysa
ba gara na mutu Momy. Dama kin jima
min Haysam da zurl'ar sa ba kaunata suk
shi naga tabbas, tunda har zai iya yima wata ciki
bani ba, shekara nawa Momy? Shekara nawa ina
cikin damuwar rashin haihuwa da rokonsa muje
muga likita amma yaki, shine yanzu za'a ce min
yar cikina nada cikinsa, Momy gara na mutu dajin
wannan mummunar magan....."
Cikin karajin itama Hajiya Hasiba ta jari
numfashinta. "Idan kin kashe kanki a tunanini
waye yaci nasara Nabeeha? Haysam ne da
janginsa. Kalli kiga, dube su kiga yanda suke cikin
dube shi kina magana bashi da lokacin baki amsa,
shin wannan bai isa ki gane abinda k**e shirin yi
bashi bane mafita?." yanda tai maganar da nuna
su Mammah ya saka Ammar zaburowa, amma sai
Mammah ta rike shi tana mai kallon Hajiya Hasiba
ido cikin ido. Cikin nutsuwarta da Dadah ya gada
ta dan girgiza kanta da murmurshin takaici.
"Kada kiyi wannan kuskuren Hajiya Hasiba. Dan
zai iya zama mafi girman abinda zai saka ki dana
sani. Ki sani ba'a gyara barna da barna, kada
kuma kiyi amfani da son zuciyarki wajen yaudarar
ta. Yin hakan a karshe dana sani yake zama
sak**akon, kuma ke zata kalubalanta. Ki gayama
Nabeeha gaskiya, ita haihuwa ta ALLAH ce Shi ke
badawa a lokacin da yaso, ga kuma war de as?).
Dan Nimrah ta samu karuwa da Muhammad basn
ke nufin ya zabeta bane da wannan matsayin bisa
nashi tsarin, ba kuma haka na nufin Nabeeha
bazata taba samu ba itama, UBANGNI ya fimu
sanin abinda ke boye......"
"Ya boye ko kuka boye? Wayama sani ko wa
abun kukai mata dan kada ta haihun da shi
ba kaunarta kuke ba? Idan ma haka ne
kun gama biyana, dan dana hafa zuri'ata
makiyyata gara ace Nabeeha ta mutu bata hainu
ba. Kuma wlhy a wannan karon dole Haysam ya
sakar min yata, idan ba haka ba kotu ce zata raha
mu".
"Hasiba kenan naji ni makiyarki ce yanda kikace
din, sannan har yanzu baki gama sanin wacece
A'isha ba wlhy, amma a wannan gabar zan
tabbatar miki da ainahina. Ni kuma idan har nice
na dauki cikin Muhammad tsawon watanni, nai
wahalar nakudar haihuwarsa, sannan na shayar
da shi da ruwan jikina bazai taba sakin Nabeeha
ba sai dai ki mutu da wannan bakin cikin. Domin
shine burinki da bazai taba cika ba, sai dai ki
cigaba da jiran lokaci. Halayen banza kuwa kada ki
fasa koya mata, kece zata kalubalanta watarana,
amma jinin Nasiru da Abdul-rasheed har abada
ya kullu a karkashin inuwar aure kenan babu
rabuwa. Dan in har kikaga hakan ta faru sai idan
a dalili daya. Ko na mutu, ko Muhammad ya mutu
Nabeeha ta masa takaba. Ko ita ta mutu ya mata.
wanka ya sallaceta..."
"Wlhy baki isa ba A'isha. Idan kina ganin kinci
nasara a baya na saka Nasir bama danki auren
Nabeeha saboda kin masa asiri keda mataccen
mijinki, sannan kin aura masa wata yar iska ni
kuma a yanzu zan tabbatar miki da ni Hasiba KIDA
A RUWA ce."
"Mi zai hana mu zuba ni da ke to Hasiba".
"Haka kika ce? To shike nan mu zuba din, ni kuwa
zan tabbatar miki nima nice na haifi Nab
k**ar yanda k**e ikirarin kin haifi naki da
"Ni da ke dan halak ka fasa".
Mammah ta fada cikin kakkausan lafazi tana
juyawa da nufin barin falon. Daga kafarta kuma
dai-dai da fasa ihun Ismat da Amimah suna kwala
kiran sunan Nabeeha da takai robar Hypo din na
kan bakinta........✍✍