AGIBASA-Hausa

AGIBASA-Hausa Wannann ingantaciyar cibiyar habbaka kasuwanci ce dake bunkasa tattalin arzikin ga Al'ummar duniya.
(1)

Saboda haha taken wannan cibiya shi ne : Mai nema na tare da samu...
An wallafa wannan cibiya ce ran 02/01/2025 Allah sa mu dace...

Wallahi Tallahi zan iya sadaukar da Aljannata ga Tinubu ni naje wuta saboda qaunar da nake masaInji matashi Lameer Abuba...
22/05/2026

Wallahi Tallahi zan iya sadaukar da Aljannata ga Tinubu ni naje wuta saboda qaunar da nake masa

Inji matashi Lameer Abubakar

“Ni mai dalilin aure, na kammala idda, ina neman miji wanda zai riƙe ni tsakani da Allah, amma banda ɗan Najeriya.”
21/05/2026

“Ni mai dalilin aure, na kammala idda, ina neman miji wanda zai riƙe ni tsakani da Allah, amma banda ɗan Najeriya.”

Gwamnatin Tarayya Ta Karyata Raɗe-Raɗin Canza Sunan Najeriya Da Soke Shari’ar Musulunci A Arewacin Nijeriya Fadar Shugab...
21/05/2026

Gwamnatin Tarayya Ta Karyata Raɗe-Raɗin Canza Sunan Najeriya Da Soke Shari’ar Musulunci A Arewacin Nijeriya

Fadar Shugaban Kasa ta karyata wani rahoto da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu na shirin sauya sunan Najeriya zuwa “United States of Nigeria” tare da soke dokar Shari’a a Arewacin kasar.

A cikin wata sanarwa da Mai Bai Wa Shugaban Kasa Shawara Kan Harkokin Yada Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ya fitar ranar 21 ga watan Mayun 2026, gwamnatin ta bayyana rahoton a matsayin “labarin karya” da wasu ke yadawa domin haddasa rikici da tayar da hankalin jama’a gabanin babban zaben 2027.

Sanarwar ta ce babu wani kudiri da Shugaba Tinubu ke shirin aikewa Majalisar Dokoki ta Kasa mai suna “Project True Federation” kamar yadda ake yadawa.

Fadar shugaban kasar ta zargi masu yada rahoton da kokarin haifar da rabuwar kai da rikicin siyasa a kasar.

“’Yan Najeriya su yi watsi gaba daya da wannan labari saboda masu yada shi makiyan zaman lafiya ne kuma masu neman tayar da tarzoma,” in ji sanarwar.

Gwamnatin ta kuma bayyana cewa sauya kundin tsarin mulkin kasa ba abu ne da shugaban kasa ko majalisa za su yi kai tsaye ba, domin akwai matakai masu tsauri da s**a hada da samun amincewar kashi biyu bisa uku na majalisun dokokin kasar da kuma majalisun dokokin jihohi 24.

Sanarwar ta ce Shugaba Tinubu na mayar da hankali ne wajen aiwatar da gyare-gyaren tattalin arziki da gwamnatin sa ta fara domin inganta rayuwar ’yan Najeriya.

Fadar shugaban kasar ta gargadi jama’a da su rika taka-tsantsan wajen karanta da yada rahotannin karya musamman yayin da harkokin yakin neman zabe ke kara karatowa.

INA KIRA GA MANYAN AREWATsohon Shugaban Mulkin Sojan Nigeria General Ibrahim Badamasi Babangida, yayi kira ga shugabanni...
21/05/2026

INA KIRA GA MANYAN AREWA

Tsohon Shugaban Mulkin Sojan Nigeria General Ibrahim Badamasi Babangida, yayi kira ga shugabannin Arewa da su hada kai domin ceto yankin daga rugujewa

A cikin wani jawabi da ya gabatar da safiyar yau, Babangida ya bayyana cewa manyan Dattawan Arewa na ci gaba da mutuwa, akwai bukatar su gyara Arewa kafin su kare

“Kun ga yadda manyan Dattawan yankin Arewa suke ta mutuwa ciki har da manyan Malamai, ‘yan siyasa, da sauransu, ni kaina yanzu karfina ya kare, kuma ina ji a raina ba zai kai karshen wannan shekara ba zan mutu, fatana a yanzu shine na cika da imani, in ji Babangida

Ya kara da cewa; a lokacin da suke mulki, sun yi duk mai yiwuwa domin tabbatar da ci gaban Arewacin Nigeria, yana mai bayar da misalin mayar da Babban Birnin Tarayya daga Lagos zuwa Abuja.

Da ace na bar Babban Birnin Tarayya a Lagos ban mayar da shi kusa da yankinmu na Arewa ba, watakila yau ba za'a ma san Arewa yadda aka santa yanzu ba, inji Shugaba Babangida

Alhamdulillah, mun yi namu bangaren, kuma lokacinmu yana karewa. Ina rokon shugabannin Arewa da su hada kai su farfaɗo da wannan yankin namu, domin ba mu da wani kamarsa, inji tsohon Shugaban Kasa Babangida

Sai dai wani babban abin takaici; daya daga cikin Dattawan Arewa mai tarin mabiya ya koma bangaren 'yan awaren Biafra don su karbi mulki su karasa ruguza Arewa

Muna cigaba da rokon Allah Ya nesanta 'yan Biafra daga mulkin Nigeria.

Me zaku iya cewa?

With AGIBASA-Hausa – I've just made it onto their weekly engagement list by being one of their top engagers!
20/05/2026

With AGIBASA-Hausa – I've just made it onto their weekly engagement list by being one of their top engagers!

YANZU-YANZU : Kotu ta bayar da belin Nasir El-Rufai kan kuɗi Naira miliyan 100.Mai shari’a Joyce Abdulmalik, a hukuncint...
18/05/2026

YANZU-YANZU : Kotu ta bayar da belin Nasir El-Rufai kan kuɗi Naira miliyan 100.

Mai shari’a Joyce Abdulmalik, a hukuncinta, ta bayyana cewa wanda zai tsaya masa a matsayin wanda zai karbi belinsa dole ne ya kasance mazaunin yankin Maitama ko Asokoro da ke Abuja sannan kuma ya ajiye asalin takaddar mallakar fili a rajistar kotu.

Me za ku ce?

BABBAR MAGANA : Wata budurwa ta rasa aikin da ake biyanta sama da naira dubu 200 a wata bayan ta ki amincewa da cire hij...
18/05/2026

BABBAR MAGANA : Wata budurwa ta rasa aikin da ake biyanta sama da naira dubu 200 a wata bayan ta ki amincewa da cire hijabinta kamar yadda kamfanin da take aiki ya bukata.

Lamarin ya jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta, inda mutane da dama ke yabawa matashiyar bisa tsayawa kan addininta da mutuncinta duk da rasa damar aikin.

Yayin da wasu ke ganin ya kamata a mutunta ‘yancin addini a wuraren aiki, wasu kuma sun bayyana cewa kamfanoni na da dokoki da ma’aikata ke bi.

Mutane da dama sun yi mata addu’ar Allah Ya maye mata da aikin da ya fi wannan alheri da albarka. 🤲

Wanne fata za ku yi mata?

Ku shiga shafin jaridar AGIBASA-Hausa domin samun Sahihan Labarai.

Dan Allah ku taya mu da sharing zuwa groups...
Sanarwa domin samun ingantattun labarai kuyi Following na:
ALPU Hausa
Madubin Bauchi
Nigeria Hausa
Madubin Arewa TV
Madubin-Fasaha
Sahihiyata
Madubin Arewa
ANNUR-Hausa
ALIB Hausa
Duniyar-Sirrin-Waya
AGIBASA-Hausa
fans

TABDIJAN: Babu wanda ya kai Tinubu nagarta a cikin 'yan siyasar da ke neman mulki a Nijeriya yanzu haka  -Inji Mawaki Am...
18/05/2026

TABDIJAN: Babu wanda ya kai Tinubu nagarta a cikin 'yan siyasar da ke neman mulki a Nijeriya yanzu haka -Inji Mawaki Aminu Ala

Daga Ayau news// Sadiya Yusuf

Mawaƙi Aminu Ladan Abubakar (Ala) ya bayyana cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya fi dukkan sauran 'yan siyasar da ke neman mulki a Nijeriya jajircewa da juriya, inda ya ƙara da cewa matakin cire tallafin fetur da shugaban ya ɗauka daidai ne domin ceto tattalin arzikin ƙasa.

Kun yarda da ALAN WAKA ?

An tabbatar da ganin jinjirin watan Zul Hijja na shekarar 1447 a ƙasar Saudi Arabia, wanda hakan ke nuna cewa watan mai ...
18/05/2026

An tabbatar da ganin jinjirin watan Zul Hijja na shekarar 1447 a ƙasar Saudi Arabia, wanda hakan ke nuna cewa watan mai alfarma zai fara daga daren jiya Lahadi .

Bisa ga sanarwar, za a gudanar da bikin Babbar Sallah ranar Laraba 27 ga watan Mayun 2026.

DA DUMI-DUMI: Kotun Koli ta Saudiyya ta bukaci a fara duba watan Babbar Sallah YauKotun Koli ta ƙasar Saudiyya ta buƙaci...
17/05/2026

DA DUMI-DUMI: Kotun Koli ta Saudiyya ta bukaci a fara duba watan Babbar Sallah Yau

Kotun Koli ta ƙasar Saudiyya ta buƙaci a fito domin duban Watan Zul-Hijja shekarar 1447, daga gobe Lahadi, 17 ga Mayu, 2026.

Kotun Kolin Saudiyya ta yi kira ga dukkan ‘yan ƙasa da mazauna ƙasar da su shiga cikin aikin duban sabon wata domin tabbatar da fara duban sabon watan Hijira na 1447.

Sanarwar ta jaddada muhimmancin watan Zul-Hijja a addinin Musulunci. A wannan wata mai alfarma ne miliyoyin Musulmai daga sassa daban-daban na duniya ke taruwa a birnin Makkah domin gudanar da aikin Hajji, wanda yana daga cikin rukunnan Musulunci guda biyar.

Hakazalika kuma, ranar goma ga watan Zul-Hijja ita ce ranar Babbar Sallah, wato Eid al-Adha, babbar ranar Idi.

Shugaba Tinubu Ya Kawo ƙarshen Talauci A Fannin Ilimi A Najeriya babu talakan da bai zuwa makaranta sabo da talauci — Mi...
17/05/2026

Shugaba Tinubu Ya Kawo ƙarshen Talauci A Fannin Ilimi A Najeriya babu talakan da bai zuwa makaranta sabo da talauci — Minista

Ministar Ƙaramar Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, Farfesa Suwaiba Sa’id Ahmad, ta ce gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta kawo ƙarshen matsalar da ke hana ‘ya’yan talakawa samun ilimi a Najeriya.

Ministar ta bayyana cewa gwamnatin Tinubu ta samar da rancen karatu, tallafin makaranta da kuma shirye-shiryen horas da matasa sana’o’i domin tabbatar da cewa babu ɗalibin da zai bar karatu saboda rashin kuɗi.

Ta ce a ƙarƙashin shirin Renewed Hope Agenda, gwamnati na ƙoƙarin bai wa matasa damar samun ilimi da ƙwarewar dogaro da kai, domin rage zaman banza da talauci a ƙasar nan.

Sai dai furucin na zuwa ne a daidai lokacin da ‘yan Najeriya ke kokawa kan tsadar rayuwa da wahalar tattalin arziki, lamarin da ya sa mutane da dama ke ganin har yanzu talauci na ci gaba da hana wasu yara zuwa makaranta.
Me zaku iya cewa?

Address

Agibasahausa
Abuja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AGIBASA-Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share