AGIBASA-Hausa

AGIBASA-Hausa Wannann ingantaciyar cibiyar habbaka kasuwanci ce dake bunkasa tattalin arzikin ga Al'ummar duniya.
(1)

Saboda haha taken wannan cibiya shi ne : Mai nema na tare da samu...
An wallafa wannan cibiya ce ran 02/01/2025 Allah sa mu dace...

Muhawara: Idan aka ba ku damar zama fuska da fuska da Shugaba Tinubu, wace shawara guda daya za ku ba shi?.  Kuyi follow...
23/08/2026

Muhawara: Idan aka ba ku damar zama fuska da fuska da Shugaba Tinubu, wace shawara guda daya za ku ba shi?. Kuyi following na AGIBASA-Hausa
fans

RAHOTO: ADC Ta Soki Kwamitin Kamfen na Tinubu, Ta Ce Sabon Dama Akabawa Masu Cin Hanci Su Cigaba Da BarnaJam’iyyar ADC t...
23/08/2026

RAHOTO: ADC Ta Soki Kwamitin Kamfen na Tinubu, Ta Ce Sabon Dama Akabawa Masu Cin Hanci Su Cigaba Da Barna

Jam’iyyar ADC ta zargi Shugaba Bola Tinubu da mayar da kwamitin yakin neman zabensa na 2027 wajen bai wa masu fuskantar zarge-zargen cin hanci wata sabuwar dama. Jam’iyyar ta bayyana damuwa kan sanya Betta Edu da Ngozi Olejeme cikin kwamitin.

ADC ta bukaci gwamnati ta bayyana halin da ake ciki kan zarge-zargen da ake wa mutanen, tana mai cewa idan an wanke su daga laifi, a bayyana yadda hakan ta faru. Ta kuma ce zaben 2027 zaizama gwaji kan ayyukan gwamnatin Tinubu. Jam’iyyar ta ce APC ba za ta iya boye matsalar tsadar rayuwa da talauci da yakin neman zabe ba.

ME ZAKU CE?

Tsohon Shugaban Hafsoshin Sojojin NajeriyaLaftanar Janar Tukur Buratai ya yi kira ga ’yan Najeriya da su yi watsi da duk...
23/08/2026

Tsohon Shugaban Hafsoshin Sojojin Najeriya
Laftanar Janar Tukur Buratai ya yi kira ga ’yan Najeriya da su yi watsi da duk wani tsoma bakin ƙasashen waje dangane da zargin da aka yi wa Shugaba Bola Tinubu kan wani lamari na miyagun ƙwayoyi da ya shafe shekaru 33.

Buratai ya yi wannan kiran ne dangane da shirin wata kotun Amurka na yanke hukunci kan sakin wasu takardu da ake zargin suna da alaƙa da wani binciken miyagun ƙwayoyi da ya shafi Shugaba Bola Tinubu sama da shekaru 30 da s**a gabata.

A wata takarda da ya fitar mai taken “Nigeria First: A Case for Protecting National Sovereignty and Dignity,” Buratai ya ce bai kamata a mayar da batun zuwa rikicin siyasa ko na mutum ɗaya ba, domin duk wani abu da zai lalata martabar Shugaban Ƙasa na iya shafar martabar Najeriya gaba ɗaya.

Ya kuma yi kira ga gwamnati da ta yi amfani da hanyoyin diflomasiyya da na shari’a wajen kare muradun ƙasa, yana mai cewa “martabar Najeriya abin karewa ce, kuma ’yancin kan ƙasar ba abin tattaunawa ba ne.”

Me zaku iya cewa?

Tsohon Gwamnan Jihar Bauchi kuma Shugaban Renewed Hope Initiative na Shiyyar Arewa maso Gabas, Malam Isa Yuguda, ya naɗa...
23/08/2026

Tsohon Gwamnan Jihar Bauchi kuma Shugaban Renewed Hope Initiative na Shiyyar Arewa maso Gabas, Malam Isa Yuguda, ya naɗa wasu mutane biyu da za su taimaka masa wajen harkokin yaƙin neman zaɓe, yaɗa manufofin Renewed Hope, da kuma neman nasarar Jam’iyyar APC a zaɓen 2027 a shiyyar.

Waɗanda aka naɗa sun haɗa da:
Salisu Ahmad Barau — S.A Media and Communication.

Dr. Aminu Gwandu — S.A Civil Society Organizations and Support Groups.

A cewar bayanin, mutanen biyu sun daɗe tare da Malam Isa Yuguda tun lokacin da yake Gwamnan Jihar Bauchi, har zuwa yanzu.

An bayyana naɗin a matsayin wani mataki na ƙarfafa ayyukan yaɗa manufofin Renewed Hope da kuma faɗaɗa harkokin wayar da kan jama’a a shiyyar Arewa maso Gabas gabanin zaɓen 2027.
Allah Ya sanya alheri. Amin.

Daga Mal. Abdul Danja, P.A. to Mal. Isa Yuguda, Pro-Chancellor, NOUN & Coordinator, Renewed Hope Initiative North East.

“Za mu tabbatar Bola Tinubu ya lashe zaɓen shekarar 2027.” Sen. Abdul'aziz Yari.Tsohon gwamnan jihar Zamfara kuma Sanata...
23/08/2026

“Za mu tabbatar Bola Tinubu ya lashe zaɓen shekarar 2027.” Sen. Abdul'aziz Yari.

Tsohon gwamnan jihar Zamfara kuma Sanata mai wakiltar al'ummar Zamfara ta Yamma a majalisar dattijan Najeriya, Sen. Abdul'aziz Yari, ya ce za su tabbatar shugaban ƙasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu yayi nasara a zaɓen 2027.

Sanata Yari, ya faɗi hakan ne a cikin saƙon godiya da ya aikewa shugaban ƙasa Bola Tinubu a yau Asabar 23rd ga watan Agustan 2026.

A jiya ne dai shugaba Tinubu ya naɗa Sen. Abdul'aziz Yari a matsayin babban daraktan yaƙ!n neman zaɓen sa na shekarar 2027 mai zuwa.

AGIBASA-Hausa
fans

"A jihar Kano akwai yankin da ba ka isa ka je ka yi maganar wata jam’iyyar ba, in ba APC ba."Hon. Jibril Isma'ila Falgor...
18/08/2026

"A jihar Kano akwai yankin da ba ka isa ka je ka yi maganar wata jam’iyyar ba, in ba APC ba."

Hon. Jibril Isma'ila Falgore, Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano.

Fitaccen jrumin Kannywood Musa mai sana'a ya ɗauki zafi sosai bayan dukan da ya sha a jihar Katsina jarumin yace tallar ...
18/08/2026

Fitaccen jrumin Kannywood Musa mai sana'a ya ɗauki zafi sosai bayan dukan da ya sha a jihar Katsina jarumin yace tallar Tinubu babu fashi inda ya aike da zazzafan saƙo zuwa ga Katsinawa.

Address

Agibasahausa
Abuja

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when AGIBASA-Hausa posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share