06/08/2026
SAUDIYA TAZAMA ABAR FARMAKAR YEN GWAGWARMAYAR HUTHI
Mai magana da yawun rundunar sojin Ansarullah (Houthiyawa) ya bayyana cewa:
Mun gano cewa Saudiyya tana wani babban shirin sojoji, da kuma shirye-shiryen ƙara kai hare-hare kan lardunan da suke ƙarƙashin ikonmu da kuma al'ummar Yemen, domin tilasta musu, su janye daga matsayinsu na neman kawo ƙarshen takunkumin zaluncin da saudiyya ta sanya musu.
Saboda haka, rundunoninmu sun gudanar da wani babban farmakin soja mai inganci, inda s**a kai hari kan wuraren da sojojin Saudiyya s**a taru a yankunan Al-Ruwayk, Al-Abr, Al-Thaniyah da wasu sansanonin da ake kira da Runduna ta Farko, da Runduna ta Uku ta Gaggawa, ta hanyar harba makamai masu linzami, (ballistic missiles) da kuma jiragen sama marasa matuƙi (drones).
A cewar sanarwar, harin ya yi sanadin mutuwa da raunata ɗaruruwan mayaƙan Saudiyya dake shirin farmakar kasarmu, tare da lalata da ƙona sansanoni, wuraren taruwar sojoji, rumbunan makamai da wasu kayan yaƙi a yankin Al-Wadiah da ke gabashin ƙasar.
Muna gargaɗin gwamnatin Saudiyya da kada ta sake aikata wani abin da zai ƙara tayar da rikici a kan ƙasarmu da al'ummarmu, domin za ta fuskanci sakamako kan duk wani matakin da za ta ɗauka.
Haka kuma muna ba waɗanda aka yaudara daga cikin 'yan ƙasarmu shawarar su bar sansanonin da ke tare da Saudiyya su koma yankunansu kafin lokaci ya ƙure musu.
Muna kira ga dukkan al'ummar ƙasarmu da su ci gaba da kasancewa cikin shirin ko-ta-kwana, tare da fuskantar duk wani hari daga Saudiyya da kuma kai farmaki kan wuraren da sojojin Saudiyya s**a taru duk inda suke.
Fassarar rahoto
Muhammad shahid Habib Al-mashastofy