23/08/2026
🇳🇬 NAF ta ƙaddamar da Operation HANUN KARFE a Arewa maso Yamma
Rundunar Sojin Sama ta Najeriya (NAF) ta ƙaddamar da wani sabon samame mai suna Operation HANUN KARFE, domin ƙara matsa lamba kan ƙungiyoyin ’yan ta’adda da sauran masu aikata laifuka a yankin Arewa maso Yamma.
NAF ta ce aikin zai mayar da hankali wajen ragargaza hanyoyin sadarwa da sansanonin ’yan ta’adda, dakile ayyukansu da hana su samun damar gudanar da hare-hare cikin sauƙi.
Rundunar ta bayyana cewa za ta gudanar da aikin ne tare da haɗin gwiwar sauran rundunonin tsaro da hukumomin da abin ya shafa, domin kare rayukan jama'a da dukiyoyinsu tare da dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.
NAF ta kuma jaddada cewa za ta yi amfani da ƙarfin jiragen yaƙi cikin tsari mai hankali da alhaki, tare da bin matakan da s**a dace wajen rage haɗarin cutar da fararen hula.
Muna fatan Allah yasa wannan shiri yazama dalilin samun zaman lafiyan yakinmu na arewa 👏
✍️ KARI GIDA NEWS ✅