KARI GIDA

KARI GIDA Wannan shafi mai suna KARI GIDA zakasamu ingatattun labarai na Ilmantarwa, nishandantarwa, kayatarwa dakuma abinda yashafi kasuwanci harda bangaren addini

🇳🇬 NAF ta ƙaddamar da Operation HANUN KARFE a Arewa maso YammaRundunar Sojin Sama ta Najeriya (NAF) ta ƙaddamar da wani ...
23/08/2026

🇳🇬 NAF ta ƙaddamar da Operation HANUN KARFE a Arewa maso Yamma

Rundunar Sojin Sama ta Najeriya (NAF) ta ƙaddamar da wani sabon samame mai suna Operation HANUN KARFE, domin ƙara matsa lamba kan ƙungiyoyin ’yan ta’adda da sauran masu aikata laifuka a yankin Arewa maso Yamma.

NAF ta ce aikin zai mayar da hankali wajen ragargaza hanyoyin sadarwa da sansanonin ’yan ta’adda, dakile ayyukansu da hana su samun damar gudanar da hare-hare cikin sauƙi.

Rundunar ta bayyana cewa za ta gudanar da aikin ne tare da haɗin gwiwar sauran rundunonin tsaro da hukumomin da abin ya shafa, domin kare rayukan jama'a da dukiyoyinsu tare da dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

NAF ta kuma jaddada cewa za ta yi amfani da ƙarfin jiragen yaƙi cikin tsari mai hankali da alhaki, tare da bin matakan da s**a dace wajen rage haɗarin cutar da fararen hula.

Muna fatan Allah yasa wannan shiri yazama dalilin samun zaman lafiyan yakinmu na arewa 👏

✍️ KARI GIDA NEWS ✅

23/08/2026

Sakone na musamman katsaya kasaurara domin kafadawa wanda baijiba Allah tsare 👏

KA KARANTA WANNAN SAI KA YI HUKUNCINi ba malami ba ne, amma ina kalubalantar duk masu tallata gwamnatin Tinubu da su kaw...
23/08/2026

KA KARANTA WANNAN SAI KA YI HUKUNCI

Ni ba malami ba ne, amma ina kalubalantar duk masu tallata gwamnatin Tinubu da su kawo hujjoji kan adalci da kyakkyawan shugabanci, ba wai kawai su dogara da cewa shugaban Musulmi ne mataikinsa ma musulmi bane ko ya furta “Lā ilāha illallāh, Muḥammadur Rasūlullāh” ba.

Ibn Taymiyyah ya kawo wata magana mai muhimmanci a Majmūʿ al-Fatāwā:

«إن الله يقيم الدولة العادلة وإن كانت كافرة، ولا يقيم الظالمة وإن كانت مسلمة»
Ma’ana:
“Allah yana tsayar da daula mai adalci ko da kuwa kafira ce, kuma ba Ya tsayar da daula azzaluma ko da kuwa Musulma ce.”
Ibn Taymiyyah ya kuma bayyana cewa al’amuran duniya suna samun daidaito da adalci, domin adalci shi ne ginshiƙin daidaituwar al’umma.

Allah kuma Ya ce:

﴿وَمَا كَانَ رَبُّكَ لِيُهْلِكَ الْقُرَىٰ بِظُلْمٍ وَأَهْلُهَا مُصْلِحُونَ﴾
(Hūd: 117)

Saboda haka, mu daina mayar da siyasa ta zama batun sunan Muslim Muslim tickets.Ka auna shugabanci da adalci, gaskiya, kare haƙƙin jama'a, tsaro da yadda ake tafiyar da dukiyar ƙasa.

Danhaka ku kyalemu muyi siyasa idan Tinubu ne alkairi Allah ya maimaitamasa mulkinsa idan kuma ba alkairi bane Allah ya canja mana shi

✍️ KARI GIDA NEWS ✅

23/08/2026

Shawara kyauta

23/08/2026

Wannan shine magana kawai

22/08/2026

Allah yasaka da alkairi Malam

Allah yasakawa malam da alkairi 🤲
22/08/2026

Allah yasakawa malam da alkairi 🤲

Congratulations Aramma!

Yanzu Alaramma Zahraddeen Adam yake sanar dani cewa Malam Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum ya biya masa aikin HAJJI. Allah yasakawa Malam da alkhairi

Yanzu haka ana ta cece-kuce kan maganar Atiku Abubakar, inda ya ce zai dawo da tallafin man fetur idan Allah Ya ba shi d...
22/08/2026

Yanzu haka ana ta cece-kuce kan maganar Atiku Abubakar, inda ya ce zai dawo da tallafin man fetur idan Allah Ya ba shi damar mulkar Najeriya. Wasu daga cikin ’yan Najeriya suna murna da wannan magana, yayin da wasu kuma suke cewa ba sa bukatar a dawo da tallafin man fetur.

To, abin da wasu ba sa gani shi ne, wadanda s**a fi amfana da cire tallafin man fetur su ne masu hali da masu manyan motoci, shi ya sa ba sa son a dawo da shi.

Amma gaskiyar magana ita ce: an cire tallafin man fetur, amma har yanzu ba a inganta albashin ma’aikata yadda ya kamata ba.

Yanzu mu tambayi kanmu: Naira ₦70,000 za ta iya daukar nauyin mutum mai iyali, matarsa da ’ya’yansa a cikin halin da ake ciki a Najeriya?

Mu a matsayinmu na ’yan Najeriya, muna bukatar a duba halin da talaka yake ciki. Idan dawo da tallafin man fetur zai rage wa talaka nauyin rayuwa, to ya kamata a sake duba batun.

Domin a karshe, abin da muke bukata shi ne mulkin da zai saukaka wa talaka rayuwa, ba wanda zai kara masa nauyi ba.

Allah ya bamu Shugaban dayake kaunarmu ba wanda muke ƙaunarsaba 🇳🇬👏

21/08/2026

Address

Abuja Kubwa Dutse Market
Abuja
POSTALCODE900001

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when KARI GIDA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share

Category