KARI GIDA

KARI GIDA Wannan shafi mai suna KARI GIDA zakasamu ingatattun labarai na Ilmantarwa, nishandantarwa, kayatarwa dakuma abinda yashafi kasuwanci harda bangaren addini

25/06/2026

"Majalisar Dokoki ta Ƙasa yanzu ta fi yin biyayya fiye da gudanar da bincike."

Ko a salon labarai:
Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya ce: "Majalisar Dokoki ta Ƙasa yanzu ba ta mayar da hankali kan sa ido da bincike kan ayyukan gwamnati ba, sai dai yin biyayya."

Follow KARI GIDA NEWS ✅

PANTAMI YA KARƁI FOM ƊIN INEC DON CIKA BAYANAN TAKARARSABayan gabatar masa da takardar shaidar Nasara (Certificate of Re...
25/06/2026

PANTAMI YA KARƁI FOM ƊIN INEC DON CIKA BAYANAN TAKARARSA

Bayan gabatar masa da takardar shaidar Nasara (Certificate of Return) a jiya Laraba a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a Jihar Gombe, Professor Isa Ali Pantami ya karɓi fom ɗin tantancewa da naɗin ɗan takara na Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta kasa (INEC) domin cike bayanansa na sirri da na takararsa.

An miƙa wa Farfesa Pantami fom ɗin ne jim kaɗan bayan karɓar takardar shaidar Nasararsa daga jam’iyyar. INEC ce ke bayar da wannan fom ga jam’iyyun siyasa domin gabatar da sunayen ’yan takararsu a hukumance.

An gudanar da wannan tsari a Hedikwatar Jam’iyyar PDP ta Ƙasa ƙarƙashin jagorancin shugaban jam’iyyar na Ƙasa, Abdulrahman Mohammed, tare da Sakataren Jam’iyyar na Ƙasa, Samuel Anyanwu.

Daga Abba Sani Pantami ✅

Follow KARI GIDA NEWS ✅

DA DUMI DUMI:Yayin da Rundunar Sojin Najeriya ta kafa Barikin Bataliya ta 21 a Anyigba, Jihar Kogi, ya dace a yaba da ga...
25/06/2026

DA DUMI DUMI:Yayin da Rundunar Sojin Najeriya ta kafa Barikin Bataliya ta 21 a Anyigba, Jihar Kogi, ya dace a yaba da gagarumin goyon baya da Gwamnan Jihar Kogi, Ahmed Usman Ododo, ya bayar, tare da matakan da yake ɗauka cikin gaggawa kan harkokin tsaro, waɗanda s**a zama abin koyi ga sauran gwamnoni.

Matakan gwamnan na nuna muhimmancin haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da hukumomin tsaro wajen tabbatar da zaman lafiya da kare rayuka da dukiyoyin al'umma.

Follow KARI GIDA NEWS ✅

Jami’an Tsaro Sun Cafke Mutum Dauke da Kayayyakin da Ake Zargin Za a Kai wa Ƴan Bindiga a Hanyar Gusau–SokotoYanzu dan A...
25/06/2026

Jami’an Tsaro Sun Cafke Mutum Dauke da Kayayyakin da Ake Zargin Za a Kai wa Ƴan Bindiga a Hanyar Gusau–Sokoto

Yanzu dan Allah idan yakai wannan kayan aka cutarda yan uwansa da danginsa a rikita kasarsa kawai dan neman abin duniya?

kai Allah yayai wadaran naka ya lalace 👏

ya Allah duk mai hannu acikin wannan cutarwa da akewa bayinka Allah karka barshi yazauna lafiya 🤲.
ya Allah karka barshi yasamu daman abinda yaribata acikin wannan matsalar 🤲

ya ka isarmana da gaggawa 🤲

follow KARI GIDA NEWS ✅

DA DUMI DUMI: Sojojin Najeriya da ke yaki da Boko Haram a yankin Arewa maso Gabas sun fito fili sun nuna rashin amincewa...
25/06/2026

DA DUMI DUMI: Sojojin Najeriya da ke yaki da Boko Haram a yankin Arewa maso Gabas sun fito fili sun nuna rashin amincewa da wani umarni da ake zargin an bayar na sake tura wasu tsoffin 'yan ta'adda da s**a tuba cikin ayyukan soji.

Sojojin sun yi gargadin cewa tilasta musu yin aiki tare, musayar bayanan sirri, ko zama tare da tsoffin masu tayar da kayar baya na iya haifar da babbar barazana ga tsaron ayyukan soji, ciki har da yiwuwar samun masu yi wa rundunar zagon kasa da kuma fallasa sirrin tsare-tsaren yaki.

Me kukace gameda wannan lamari?
Anyakuwa bazai kawo nakaso bakuwa da ga tsarin tsaron kasar muba?

Follow KARI GIDA NEWS ✅

25/06/2026

Ga shaidar malam ta halasta tacen takarar sa ✅

Allah ya kawo nasara 🤲

Follow KARI GIDA NEWS ✅

DA DUMI DUMI: Gwamnatin Tarayya ta gano manyan ma'adanai masu muhimmanci a Jihar Kaduna, ciki har da Platinum Group Meta...
25/06/2026

DA DUMI DUMI: Gwamnatin Tarayya ta gano manyan ma'adanai masu muhimmanci a Jihar Kaduna, ciki har da Platinum Group Metals (PGM), zinariya (Gold), Nickel, Copper, Lithium da kuma Rare Earth Elements.

An bayyana cewa wannan sabon ganowan na iya sanya Najeriya cikin manyan kasashen da ke da muhimman ma'adanai da ake bukata a masana'antu da fasahar zamani a duniya.

Shin kuna ganin cewar Nigeria zata amfana da wannan ni imarkuwa?

Follow KARI GIDA NEWS ✅

25/06/2026

Allahu akbar kabiran ✅

Abin da ya sa nake goyon bayan kafa ‘yan sandan jihohi (State Police) dari bisa dari shi ne, duk da cewa ‘yan sandan da ...
24/06/2026

Abin da ya sa nake goyon bayan kafa ‘yan sandan jihohi (State Police) dari bisa dari shi ne, duk da cewa ‘yan sandan da muke da su a yanzu ba su isa ba. Jimillar ‘yan sandan Najeriya ba su kai 400,000 ba. Najeriya mai yawan al’umma sama da miliyan 200 tana bukatar akalla ‘yan sanda miliyan 1."

— Ali Ndume, Sanata.

follow KARI GIDA NEWS ✅

🏮DA DUMI DUMI: Majalisar Dattawan Najeriya ta fara kada ƙuri'a da hannu (manual voting), sashe bayan sashe, kan gyaran k...
24/06/2026

🏮DA DUMI DUMI: Majalisar Dattawan Najeriya ta fara kada ƙuri'a da hannu (manual voting), sashe bayan sashe, kan gyaran kundin tsarin mulki domin kafa 'Yan Sandan Jihohi (State Police) a Najeriya. �

Wannan mataki na nufin sanatoci suna nazartar kowace sashe ta kudirin doka tare da kada ƙuri'a a kai domin yanke hukunci kan kafa rundunar 'yan sanda ta jihohi, wadda za ta yi aiki tare da rundunar yan sandan Nigeria. 🇳🇬

Muna fatan Allah yasa wannan yunkuri yazama silar samun zaman lafiya 🤲 da kwanciyar hankali a kasar mu Nigeria 🇳🇬🤲 dama duniya baki daya 🤲

Follow KARI GIDA NEWS ✅

Address

Abuja Kubwa Dutse Market
Abuja
POSTALCODE900001

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when KARI GIDA posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category